Rana Ta 3: Masu Zanga Zanga Sun Toshe Titi Mai Muhimmanci a Abuja kan Matsalar Tsaro

Rana Ta 3: Masu Zanga Zanga Sun Toshe Titi Mai Muhimmanci a Abuja kan Matsalar Tsaro

  • Masu zanga-zanga sun toshe gadar Karu-Nyanya, sun bukaci gwamnati ta dauki mataki kan yawaitar hare-haren yan ta'adda a kasar nan
  • Hakan dai na zuwa ne yayin da zanga-zangar adawa da matsalar rashin tsaro ta shiga rana ta uku a babban birnin tarayya Abuja
  • Sha'anin tsaro na ci gaba da kara kamari a Najeriya musamman bayan sace dalibai da malamai a makarantu a jihohin Oyo da Borno

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Matasa sun sake mamaye tituna a babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja, yayin da zanga-zanga kan matsalar rashin tsaro ta shiga rana ta uku a jere.

Rahotanni sun nuna cewa masu zanga-zangar suka toshe wata gada da ke kan babban titin Karu-Nyanya, lamarin da ya haifar da cunkoson ababen hawa.

Zanga zanga.
Masu zanga-zanga sun mamaye titin Karu-Nyanya da Shugaba Bola Ahmed Tinubu Hoto: @BigJunior5, @aonanuga1956
Source: Twitter

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa masu zanga-zangar sun fito dauke da alluna masu dauke da sakonni daban-daban tare da rera wakokin suka ga gwamnati.

Kara karanta wannan

Kotu ta yi umarni a kama tsohon ministan Tinubu da ya samu takarar gwamna

Sun bukaci hukumomi su tashi tsaye wajen cika nauyin da kundin tsarin mulki ya dora musu na kare rayuka da dukiyoyin al'ummar Najeriya.

An toshe muhimmiyar hanyar Abuja

Rahotanni sun nuna cewa masu zanga-zangar sun fara taruwa ne a kan wata gada da ke yankin Karu kafin daga bisani su fara tattaki zuwa Nyanya.

Toshe hanyar ya haifar da cunkoson ababen hawa mai tsanani a kan titin Abuja zuwa Keffi, lamarin da ya sa matafiya da dama suka makale na tsawon sa'o'i.

Masu zanga-zangar sun bayyana cewa yawaitar sace-sacen mutane, hare-haren yan ta'adda da sauran matsalolin tsaro sun sanya rayuwa ta zama mai wahala ga mazauna yankunan.

Sun bukaci gwamnati ta dauki mataki

Masu zanga-zangar sun yi kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su dauki tsauraran matakai domin dakile matsalolin tsaro da suka addabi sassan kasar nan.

Sun ce rashin tsaro ya jefa jama'a cikin fargaba tare da kawo cikas ga harkokin yau da kullum, kamar yadda Punch ta rahoto.

An tura dakarun tsaro zuwa wurin

Bayanai sun nuna cewa an jibge jami'an tsaro a yankin domin sa ido kan zanga-zangar tare da taimaka wa wajen daidaita zirga-zirgar ababen hawa.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: 'Yan fansho sun yi da na sanin tara wa gwamna kudin sayen fam

Hukumomi sun kuma bukaci masu amfani da hanyar da su nemi wasu hanyoyi na daban saboda cunkoson da zanga-zangar ta haifar.

Yan sanda.
Dakarun rundunar yan sandan Najeriya a bakin aiki Hoto: @PoliceNG
Source: Twitter

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ba a samu barkewar rikici ko asarar rai ba, sai dai har yanzu toshe hanyar na ci gaba da kawo tsaiko ga zirga-zirga a yankin Karu da Nyanya.

Wani matashi, Aminu Ahmad ya shaida wa Legit Hausa cewa ya kamata yan Arewa su dauki darasi kan gudanar da zanga-zangar lumana domin mika bukatunsu ga gwamnati.

Ya ce yan Arewa ba su iya zanga-zangar lumana da za a karelafiya ba, galibi sai an kwashi kayan mutane.

"ina fatan yan Arewa za su farka, su yi koyi da wannan zanga-zanga, sannan muna fatan hankalin gwamnati ya dawo jikinta, ta magance matsalar tsaron nan, domin abin ya wuce tunani," in ji shi.

Matawalle ya fadi hanyar dawo da tsaro

A wani labarin, kun ji cewa Karamin Ministan Tsaro na Ƙasa, Bello Matawalle, ya ce Allah SWT ne kaɗai zai iya kawo ƙarshen matsalar tsaron da ke addabar Najeriya.

Kara karanta wannan

ESN ta shirya kai hare hare a wasu sassan Najeriya, DSS, sojoji sun dauki mataki

Ya ce matsalar tsaro ta shafi kowa da kowa ba tare da la'akari da jam'iyya ko addini ba, don haka ya kamata 'yan Najeriya su haɗa kai da jami'an tsaro domin kawo ƙarshenta.

Ya ƙara da cewa babu wani ɗan Najeriya da ke farin ciki da abin da ke faruwa, amma wasu daga cikin 'yan adawa suna amfani da matsalar domin nuna gazawar gwamnati.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262