Atiku Ya Yi Murna da Ceto Mutane 360, Ya Ce Sojoji Za Su Iya Murkushe Ta'addanci a Najeriya

Atiku Ya Yi Murna da Ceto Mutane 360, Ya Ce Sojoji Za Su Iya Murkushe Ta'addanci a Najeriya

  • 'Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar ADC, Atiku Abubakar ya yi murna da ceto mutum 360 da aka sace a Ngoshe da ke jihar Borno
  • Tsohon mataimakin shugaban kasar ya yabawa sojoji da jami’an tsaro kan nasarar da suka samu na ceto mutanen bayan watanni fiye da biyu
  • Ya ce hakan ya nuna cewa dakarun tsaron Najeriya za su iya magance duk wata barazana matukar aka samar masu da kayan aiki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Borno, Nigeria - Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa kuma 'dan takarar shugaban kasa na ADC, Atiku Abubakar, ya nuna farin cikinsa kan ceto mutane 360 da aka yi garkuwa da su a Ngoshe, jihar Borno.

Atiku ya ce wannan nasara ta kawo karshen wahalar da wadanda aka sace da iyalansu suka shafe watanni suna ciki tun bayan garkuwa da su a watan Maris da ya gabata.

Kara karanta wannan

Amurka ta gamu da matsala, jirgin yakinta ya rikito a kusa da mashigar Hormuz

Atiku.
'Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar ADC a zaben 2027, Alhaji Atiku Abubakar
Source: Twitter

Hakan na kunshe ne a cikin wani sako da Atiku ya wallafa a shafinsa na X a jiya Litinin, 8 ga watan Mayu, 2026.

Atiku Abubakar ya yaba wa jami’an tsaro

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya yaba wa rundunar sojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro da suka taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da aikin ceton.

Ya ce wannan nasara ta nuna cewa jami’an tsaron kasar na da kwarewa da karfin da za su iya kawo karshen matsalar tsaro idan aka samar musu da kayan aiki da kuma ingantaccen shugabanci.

A cewarsa, rikicin ta’addanci da ya addabi Najeriya tsawon kusan shekaru 20 zai iya zama tarihi idan aka kara bai wa jami’an tsaro cikakken goyon baya.

Ya bukaci a ceto daliban Oyo, Borno

Duk da yabon da ya yi kan ceto mutanen Ngoshe, Atiku ya nuna cewa har yanzu akwai babban aiki a gaba saboda wasu ’yan Najeriya na ci gaba da kasancewa a hannun masu garkuwa da mutane da ’yan ta’adda.

Kara karanta wannan

Matsalar tsaro: NLC da TUC sun yi barazanar hana ma'aikata zuwa wurin aiki a Najeriya

Ya bukaci gwamnati da jami’an tsaro su kara kaimi wajen kubutar da kusan dalibai da malamai 100 da aka sace a yankin Oriire na jihar Oyo da kuma Mussa a jihar Borno.

Atiku ya ce ya kamata a yi amfani da wannan nasara a matsayin karin kwarin gwiwa wajen ceto sauran mutanen da ke tsare a hannun masu garkuwa.

Sojoji.
Dakarun sojojin Najeriya suna aikin tabbatar da tsaro a Arewa maso Gabas Hoto: @NigerianArmy
Source: Twitter

Kiran sake fasalin tsarin tsaro

Hakazalika, Atiku ya yi kira da a sake fasalin tsarin tsaron Najeriya ta yadda za a fi mayar da hankali kan tattara bayanan sirri, amfani da fasahar zamani da kuma daukar matakan kariya kafin hare-hare su faru.

Ya ce matakan kariya da gano barazana tun kafin ta afku su ne mafi dacewa wajen dakile ayyukan ’yan ta’adda da masu garkuwa da mutane a fadin kasar.

Atiku ya soki tsarin tsaron Tinubu

A wani labarin, kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya soki yadda gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke tafiyar da sha'anin tsaro.

Ya buƙaci Gwamnatin tarayya da ta hanzarta gudanar da cikakkiyar bita kan tsarin manufofin yaƙi da ta'addanci na Najeriya.

Atiku ya ce ya kamata Gwamnatin tarayya ta rika nazari tare da daukar darussa daga hare-haren 'yan ta'adda domin sauya salo da dabarun yaki da ta'addanci.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262