Labarin Sojojin Najeriya
Dakarun Najeriya sun kashe 'yan bindiga masu garkuwa da mutane a jihar Kaduna bayan wani farmaki da suka kai. Sojojin sun yi nasarar cafke mutane huɗu a Kaduna.
Dan ta'adda, Bello Turji ya bayyana cewa a shirye yake a yi zaman lafiya da shi ko kuma yaki idan aka zabi hakan. Bello Turji ya ce bai ajiye makami ba.
Wasu dakarun sojojin Najeriya sun rasa ransu sakamakon fashewar bam a jihar Sokoto. Ana zargin 'yan bindiga ne suka dasa masu bam din a kan hanya.
Iyalan jami’an sojin Najeriya da ake zargi da hannu a shirin juyin mulki sun zargi rundunar soji da cin zarafi, hana samun lauyoyi da kuma rashin bayyana gaskiya.
Ministan tsaro, Christopher Musa, ya bayyana cewa za su fara shiga wuraren yaki tare da 'yan jarida domin dauko rahotanni masu inganci da sanar da jama'a.
Gwamnatin tarayya ta bukaci yan Najeriya du rika bai wa nassrorin jami'an tsaro muhimmanci wajen yada labaransu, su kuma daina saka ayyukan yan bindiga a sahun gaba.
Tsohon shugaban hukumar NYSC, Birgediya Janar Maharazu Tsiga (mai ritaya), ya samo mafita kan matsalar 'yan bindiga da suke sace mutane zuwa cikin daji.
Tsofaffin hafsoshin soja da abokan marigayi marigayi Janar Rabe Abubakar mai ritaya sun bukaci a yi garambawul ga tsarin tsaro bayan mutuwarsa a hannun ‘yan bindiga.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa dan ta'adda, Bello Turji bai gagari hukuma ba kuma da yarfae Alah ya kusa shiga hannun jami'an tsaron Najeriya.
Labarin Sojojin Najeriya
Samu kari