Gwamnatin Tinubu Ta Kafa Tarihi, Ta Kawo Sababbin Dokoki game da Talla a Najeriya

Gwamnatin Tinubu Ta Kafa Tarihi, Ta Kawo Sababbin Dokoki game da Talla a Najeriya

  • Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da Kotun Laifukan Talla a Abuja, domin ƙarfafa tsari, sa ido da ƙwarewa a masana'antar talla
  • Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris ya buƙaci kotun ta gudanar da ayyukanta cikin gaskiya, 'yanci da adalci
  • Shugabar kotun, Cecilia Olatoregun, ta yi alƙawarin tabbatar da gaskiya da ƙwarewa, yayin da ARCON ta bayyana kotun a matsayin ta farko a duniya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da sababbin tsare-tsare game da yadda ake gudanar da talla.

An ƙaddamar da sabuwar Kotun Laifukan Talla, a wani mataki na ƙarfafa tsari da sa ido kan harkar talla, inganta ƙwarewa.

Gwamnatin Tinubu ta kafa kotu ta musamman kan talla
Shugaba Bola Tinubu na Najeriya. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Facebook

An kaddamar da kotun talla a Najeriya

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a wurin ƙaddamar da kotun a Abuja kamar yadda ma'aikatar ta wallafa a Facebook.

Kara karanta wannan

Kano ta karyata sanya wasu dattawa a auren gata, ta ba limaman Juma'a umarni

Idris ya ce manufar gwamnatin ita ce gina masana’antar talla da za ta kasance abin koyi wajen ƙirƙire-ƙirƙire, samun amincewar jama’a da kuma tabbatar da ɗaukar nauyi.

Ya ce:

“Mu gina masana'antar talla da za ta yi fice wajen ƙirƙire-ƙirƙire, ta samu amincewar jama'a kuma ta kiyaye ɗaukar nauyi."

Ministan ya bayyana cewa Dokar Majalisar Kula da Harkokin Talla ta Nijeriya (ARCON) ta shekarar 2022, mai lamba 23, ta ƙara faɗaɗa ikon hukumar wajen tsara da sa ido kan harkokin talla.

A cewarsa, dokar ta kuma tanadi kafa kotun da za ta saurari laifukan da suka shafi dokar, da kuma sauran ƙa’idoji da dokokin da ke kula da harkar talla a ƙasar.

Idris ya buƙaci sabuwar kotun, wadda Mai Shari’a Cecilia M. A. Olatoregun ke jagoranta, da ta gudanar da ayyukanta cikin gaskiya, ’yanci da adalci.

Ya ce duk wata shari’a da aka gabatar a gaban kotun ya kamata a yi hukunci a kanta bisa hujjojin da ke gabanta, ba tare da tsoro, son rai, ƙauna ko ƙiyayya ba.

Kara karanta wannan

Shugaban APC ya tona yadda yan siyasa ke gwara yan Najeriya da sunan addini

A cewarsa:

“Duk wata shari'a da aka gabatar a gaban ku, ku duba ta bisa hujjojin da ke cikin ta, ba tare da tsoro ko nuna son kai ba, ko ƙauna ko ƙiyayya. Dole kotun ta kasance, kuma a gan ta a matsayin hukuma mai adalci da rashin nuna son kai."

Ministan ya taya shugabar kotun da sauran mambobinta murna, tare da tabbatar musu cewa ma’aikatarsa za ta ci gaba da tallafa wa ARCON wajen gina masana’antar talla da za ta iya gogayya da sauran ƙasashe.

Tun da farko, Darakta-Janar na ARCON, Dakta Olalekan Olumuyiwa Fadolapo, ya bayyana kafa Kotun Laifukan Talla a matsayin wani babban ci gaba wajen ƙarfafa bin dokoki da ƙa’idoji a masana’antar talla.

Fadolapo ya ce kotun ta kasance wata babbar dama ga masana’antar talla ta Nijeriya, yana mai cewa kafa irin wannan kotu wata hanya ce ta hangen nesa wajen inganta tsarin gudanar da harkar talla.

Ya ce:

Kara karanta wannan

Tinubu ya yayyafa ruwan sanyi bayan kalaman Jingir sun ta da kura

“Kotun Laifukan Talla wata babbar dama ce ga masana'antar talla ta Nijeriya. Ita ce irin ta ta farko a duniya, domin Nijeriya ta ɗauki matakin hangen nesa, ba wai kawai wajen kafa dokoki kan harkar talla ba, har ma da samar da tsare-tsare da tsarin gudanarwa."

A nata ɓangaren, Shugabar Kotun Laifukan Talla, Mai Shari’a Cecilia M. A. Olatoregun, ta yi alƙawarin cewa kotun za ta gudanar da ayyukanta cikin gaskiya, adalci da ƙwarewa.

Ta bayyana cewa kiran su domin yi wa ƙasa hidima babban abin alfahari ne, kuma za su ɗauki nauyin da aka ɗora musu da muhimmanci.

Ta ce:

“Babban abin alfahari ne a kira mu domin yi wa ƙasar mu hidima, kuma mun ɗauki wannan nauyi da muhimmanci sosai. An buƙace mu da yin aiki cikin gaskiya, kuma wannan shi ne abin da za mu yi."

Mambobin Kotun Laifukan Talla sun haɗa da Musa Ahmed Attah, SAN; Merga Tyowanan Kachina, Esq.; Dakta Ken Onyeali Ikpe, FRPA; da Hajiya Sa’a Ibrahim, RPA.

Tinubu ya fadi yadda ake yi da bashi

Kun ji cewa Fadar Shugaban Kasa ta kare manufar karɓo bashi ta Bola Tinubu ke yi, wanda ya fara jawo maganganu daga yan adawa da masu sharhi.

Kara karanta wannan

NLC ta bude kofar tattaunawa da gwamnati, ma'aikata na iya samun karin albashi

Hadimin Shugaban kasa, Bayo Onanuga ya bayyana cewa ana ganin inda kuɗin ke tafiya ta hanyar manyan ayyukan more rayuwa.

Bayo Onanuga ya lissafo wasu ayyuka da ya kira manya-manya, wanda ya ce kadan ne daga cikin hanyoyin da Tinubu ke kashe basussukan da ya amso.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.