Hukumar Sojin Najeriya
Ana zargin Bola Tinubu ya faɗaɗa Sojojin Najeriya daga rundunoni 8 zuwa 12 tare da shirin ɗaukar sojoji 28,000 saboda tsoron juyin mulki a ƙasar.
Gwamnan Kebbi, Nasir Idris, ya bukaci sojoji su kawar da ’yan bindiga, yana mai cewa karin dakaru zai taimaka wajen dawo da tsaro da manoma gonakinsu.
Hedikwatar tsaro ta ce sojojin Najeriya sun hallaka ’yan ta’adda 69, sun ceto sama da mutane 360 da aka yi garkuwa da su tare da cafke wasu 49 cikin mako guda.
Sojoji sun hana arangama tsakanin ƴan ƙabilar Fulani da Mwaghavul a karamar hukumar Mangu, Plateau, bayan musayar wuta kusa da kauyukan Gaude da Aloghom.
Sanatocin yankin Arewa sun yabawa Tinubu da hukumomin tsaro bayan kubutar da mutanen Woro, tare da kira ga jama'a su ci gaba da ba da sahihan bayanai.
Sojoji sun yabawa Shugaba Tinubu kan karin albashi daga kashi 30 zuwa 80, tare da bukatar gwamnati ta sake duba alawus dinsu domin rage tasirin tsadar rayuwa.
Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar ya bukaci a binciki kisan Kanal Abdussalam Ude, tare da yin Allah-wadai da ƙiyayya ga Musulman Igbo tsiraru.
Rundunar sojin Najeriya ta ayyana shugaban ISWAP, Abu Musa Al-Mangawi Baa Shuwa, da mataimakinsa Muhammad Jidda a matsayin waɗanda ake nema, ta sanya ladar kudi.
Shugaba Bola Tinubu ya amince da ƙarin albashin sojojin Najeriya da ya kai tsakanin kashi 30 zuwa 80 cikin 100, wanda zai fara aiki daga ranar 1 ga Satumba.
Hukumar Sojin Najeriya
Samu kari