Akwai Matsala: Cutar Kwalara Ta Kama Mutane Sama da 4,000 a Borno, An Rasa Rayuka
- Rahotanni sun nuna cewa an samu karin mutane 274 da suka kamu cutar kwalara a cikin sa'o'i 24 da suka gabata a jihar Borno
- Bayanai daga gwamnatin Borno sun nu a cewa wadanda suka kamu da cutar ta amai da gudana sun haura 4,000, kuma 39 daga cikin sun mutu
- Gwamna Babagana Umara Zulum ya amince da raba magunguna da kayan jinya ga wuraren da ake kula da wadanda suka kamu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Borno, Nigeria - Akalla mutum 39 sun rasa rayukansu yayin da sama da mutane 4,200 ake zargin sun kamu da cutar kwalara a wasu kananan hukumomin jihar Borno.
Jami’an lafiya sun bayyana hakan ne a wani taron wayar da kai kan hanyoyin kariya da maganin zawo mai tsanani da aka gudanar a Maiduguri, babban birnin jihar.

Kara karanta wannan
'Yan bindiga sun kai mummunan hari masallaci ana tsakiyar sallar Magriba a Kaduna

Source: Original
Cutar ta harbi karin mutane 274
Rahoton Leadership ya ruwaito shugaban cibiyar harkokin gaggawa na lafiya ta jihar, Dakta Jacob Thlizer, na cewa an samu karin mutane 274 da ake zargin sun kamu da cutar cikin sa’o’i 24 kacal.
A cewarsa, adadin wadanda ake zargi da kamuwa da kwalara ya kai mutum 4,204 a unguwanni 36 da ke cikin yankunan da annobar ta shafa.
Ya bayyana cewa adadin mutanen da suka mutu ya kai 39 zuwa lokacin da aka fitar da rahoton, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.
Yankunan da annobar ta fi kamari a Borno
Dakta Thlizer ya ce cutar ta bazu zuwa kananan hukumomi da dama da suka hada da Jere, Bama, Kaga, Mafa, Kwaya Kusar, Maiduguri Metropolitan Council (MMC), Konduga, Monguno, Magumeri da Ngala.
Rahoton ya nuna cewa MMC ce ke da mafi yawan masu dauke da cutar da mutum 2,404, sai Jere da mutum 1,214.
Gwamnati ta dauki matakan gaggawa
Jami’an lafiya sun bayyana cewa gwamnatin Borno ta fara daukar matakan dakile yaduwar cutar.
Daga cikin matakan akwai kafa tsarin gudanar da ayyukan gaggawa, gudanar da taruka da abokan hulda a bangaren lafiya, wayar da kan jama'a da kuma samar da magunguna da kayan aikin jinya.

Source: Facebook
Gwamna Zulum ya ware magunguna
Sakataren ma’aikatar lafiya ta jihar, Shetima Muhammad, ya ce an ware cibiyar kula da cututtuka masu yaduwa da ke Njimtilo da kuma sansanin kula da marasa lafiya a Ngarannam mai gado sama da 1,000 domin kula da masu fama da cutar.
Ya kara da cewa Gwamna Babagana Umara Zulum ya amince da raba magunguna da kayan jinya ga wuraren da ake kula da wadanda suka kamu.
Jami’an gwamnati sun bukaci mazauna jihar su rika kula da tsaftar muhalli da ta abinci, su rika amfani da ruwa mai tsafta, sannan su garzaya asibiti idan sun fara ganin alamomin kwalara.
NCDC ta yi gargadi kan cutar Ebola
An ji cewa hukumar yaki da yaduwar cututtuka ta kasa (NCDC) ta sanya Legas, Kano, Rivers da wasu jihohi cikin shirin ko-ta-kwana kan cutar Ebola.
A cikin sanarwar lafiya ta kasa da ta aika wa kwamishinonin lafiya a fadin kasar, hukumar ta gargadi cewa Najeriya na cikin hadarin shigowar cutar.
NCDC ta ce cutar za ta iya bulla a jihohin ne saboda filayen jiragen sama na kasa da kasa da suke da shi, tashoshin ruwa, iyaka da kasashe da yawan zirga-zirgar jama’a.
Asali: Legit.ng

