Kiwon Lafiya
A labarin nan za a ji cewa Majalisar dokokin jihar Kano ta bayyana damuwa bayan cutar mashako ta yi sanadin rasuwar yara akalla 50 a karamar hukumar 1.
Cutar ido mai saurin yaɗuwa da ake kira “Apollo” ta bulla a Jihar Bauchi, inda Kakakin Majalisar Dokokin jihar, Abubakar Suleiman, ya ce ya kamu da ita.
Mutane huɗu yan gida ɗaya da karensu sun mutu bayan cin amala a Kogi. Gwamnati ta umarci Ma’aikatar Lafiya da ta binciki yiwuwar samun guba a abincin.
Daraktan UNIMEDTH, Farfesa Michael Gbala, ya yi gargadin cewa jabun magunguna na iya kashe mutane fiye da ’yan bindiga, tare da kira da a ƙara sa ido kan ingancinsu.
PHIMA ta rufe cibiyoyin lafiya masu zaman kansu 37 a Kano cikin watanni 18 saboda karya ƙa’idoji, yayin da sama da cibiyoyi 1,405 ke da rajista a jihar.
An tabbatar da cutar sake bullar Apollo a Potiskum, Yobe, yayin da mazauna suka koka kan saurin yaɗuwarta. Mahukunta sun ba da shawarwarin kariya.
Tarayyar Turai ta ware €2.3m ga Najeriya da wasu ƙasashe uku domin yaƙi da annobar kwalara, inda Najeriya za ta samu €1.5m daga cikin jimillar kudin.
Hunter Biden ya ce ciwon dajin da mahaifinsa, Joe Biden ke fama da shi ya bazu zuwa ƙasusuwansa, yana haifar masa da ciwo da raunana jikinsa gaba daya.
Gwamnatin Bauchi ta ayyana barkewar cutar kwalara bayan tabbatar da kamuwa da cutar, inda aka samu mutane 398 da ake zargi da ita da kuma mutuwar 16.
Kiwon Lafiya
Samu kari