Farfesa Rabi'a daga Kano Ta Yi Magana kan Mukamin da Aka Nada ta a Majalisar Dinkin Duniya
- Malama a jami'ar Bayero da ke Kano (BUK), FarfesaRabia Sa’id ta yi karin haske kan nadin da aka yi mata a kwamitin Majalisar Dinkin Duniya
- Martanin Farfesa Rabia na zuwa ne bayan labarin nadin da aka mata ya sake bulla a kafafen sada zumunta a Najeriya
- Rahoto ya nuna cewa an nada ta a kwamitin da zai yi nazarin illolin zahiri da na zamantakewa na makamin nukiliya a duniya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria - Farfesar Physics a Jami’ar Bayero Kano (BUK), Rabia Sa’id, ta bayyana cewa nadin da aka yi mata a Kwamitin Kimiyya na Majalisar Dinkin Duniya kan Illolin Yaƙin Nukiliya (2025–2027) ba sabo ba ne.
Wannan kalamai na zuwa ne bayan labarin nadin da aka yi mata ya sake bulla a kafafen yada labarai daban-daban a Najeriya.

Source: Facebook
A wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook da aka tabbatar, Farfesar ta ce Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya ya naɗa ta cikin kwamitin mutum 21 tun watan Disambar bara.
Nadin, wanda aka kafa bisa ƙudurin Babban Taron Majalisar Dinkin Duniya mai lamba 79/238, ya sanya Farfesa Rabia cikin manyan masana kimiyya da ke nazarin barazanar nukiliya da ka iya shafar rayuwar duniya.
Yadda aka sake yada nadin Farfesa Rabia
Wani rahoto da Premium Times ta wallafa bisa wani bayani daga BUK Media ranar Litinin ya sake jawo hankalin jama’a kan nadin nata.
Bayan wasu martani da aka samu a kafafen sada zumunta, Farfesa Rabia Sa'id ta bayyana cewa rahotannin ba sa nufin sabon nadi ' ne.
“Duk da cewa ina godiya da fatan alherinku, ya kamata a sani cewa wannan ba sabon nadi ba ne.
"Shi ne nadin da muka yi bikin sa a bara lokacin da Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya ya sanar da mambobin Kwamitin da aka lafa kan illolin yaƙi da makamin nukiliya.
“Ina ganin wani ne kawai ya sake wallafa shi, sannan aka ci gaba da yadawa har ya bazu," in ji ta.
Kwamitin ya fara aiki tun Disamba
Rabia ta ce kwamitin ya fara gudanar da aikinsa ne tun lokacin da aka kaddamar da shi a watan Disamban 2025 a hedikwatar Majalisar Dinkin Duniya da ke New York.
Ta bayyana cewa tun bayan kaddamar da kwamitin, mambobinsa sun gudanar da taruka ta yanar gizo da dama, sannan suka gudanar da wani taron kai tsaye a Vienna, Austria, a watan Maris.

Source: Facebook
Ta ce za a sake gudanar da wani taro a Geneva, Switzerland, a watan Satumba, tare da wasu tarurrukan tuntubar masu ruwa da tsaki a yankuna daban-daban kafin gabatar da rahoton ƙarshe a Taron Majalisar Dinkin Duniya a 2027.
An fara shirin zabe a Majalisar dinkin duniya
Kun ji cewa 'yan takara shida da ke neman kujerar babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya sun fara gabatar da manufofinsu a wani taron tambayoyi da aka shirya.
Majalisar Dinkin Duniya dai na fuskantar matsananciyar matsalar kudi da kuma raguwar amincewar kasashe a duniya bayan zargin fa gwamnatin Amurka ta mata.
Asali: Legit.ng

