Abu Ya Girma: Jam'iyyar APC Ta Dakatar da Dan Majalisar Tarayya daga Jihar Jigawa
- APC ta dakatar da 'dan Majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Auyo/Hadejia/Kafin Hausa, Hon. Usman Ibrahim tare da shugabanni
- Hakan ya biyo bayan korafe-korafen da aka shigar kansu cewa suna gudanar da wasu ayyuka da suka saba wa kundin tsarin jam'iyya
- APC ta umarci wadanda aka dakatar da su daina ayyana kansu a matsayin jami’ai ko wakilan jam’iyyar har sai an kammala bincike
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jigawa, Nigeria - Jam’iyyar APC reshen jihar Jigawa ta dakatar da 'dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Auyo/Hadejia/Kafin Hausa, Hon. Usman Ibrahim, daga jam’iyyar.
Shugaban APC na jihar Jigawa, Ahmad Garba, ne ya sanar da matakin cikin wata sanarwa da aka fitar ga manema labarai ranar Litinin.

Source: Twitter
A cewarsa, jam’iyyar ta dauki matakin ne bayan karbar korafe-korafe da rahotanni daga mambobinta kan zargin hannu a ayyukan da suka saba wa dokokin APC, kamar yadda Premium Times ta rahoto ba.
Dalilin APC na dakatar da dan Majalisa
Sanarwar ta bayyana cewa ana zargin 'dan majalisar da wasu shugabannin APC a matakin mazaba da kananan hukumomi da aikata abubuwan da suka ci karo da manufofi da dokokin APC.
A cewar APC, ana zargin wadanda abin ya shafa da daukar matakan da za su iya bata sunan jam’iyyar, raunana ikon shugabancinta da kuma haddasa rikici tsakanin mambobi.
“Idan aka tabbatar da wadannan zarge-zarge, tonsun saba da sashe na 21.2 na kundin tsarin mulkin APC wanda ya haramta rashin biyayya ga wata jam’iyya da ayyukan da za su jefa ta cikin matsala,” in ji sanarwar.
APC ta dakatar da wasu jiga-jigai 6
Baya ga Hon. Usman Ibrahim, APC ta kuma dakatar da wasu shugabannin jam’iyyar guda shida.
Wadanda aka dakatar din sun hada da Aisha Adamu, mataimakiyar shugabar mata ta APC a jihar Jigawa, Yargabi Babannan, shugabar mata ta mazabar Auyo, da Musa Zabarau, shugaban APC na mazabar Auyo.
Sauran sune Ibrahim Ayama, mataimakin shugaban APC na karamar hukumar Auyo. Saje Hadiyau, sakataren kudi na APC a Auyo, Sani Hadiyau, mataimakin shugaban APC na mazabar Auyo.

Source: Facebook
APC ta umarci wadanda aka dakatar da su da su daina ayyana kansu a matsayin jami’ai ko wakilan jam’iyyar har sai an kammala bincike.
Haka kuma an hana su halartar taruka ko gudanar da duk wani aiki da ya shafi APC a hukumance, tare da gargadin su da kada su yi wani abu da zai iya tasiri ga binciken da ake yi.
Asali: Legit.ng

