Rigima Ta Kunno Kai a Jam'iyyar APC, An Dakatar da Sanata Jibrin Isah

Rigima Ta Kunno Kai a Jam'iyyar APC, An Dakatar da Sanata Jibrin Isah

  • Jam'iyyar APC a mazabar Odu ta dakatar da sanatan Kogi ta Gabas, Jibrin Isah wanda aka fi sani da Echocho bisa zargin cin amana
  • Shugabannin APC na mazabar sun zargi sanatan da ganawa da jam'iyyun adawa, abin da suka ce ya saba wa kundin tsarin mulkin APC
  • A nasa bangaren, Sanata Echocho ya yi fatali da dakatarwar yana mai cewa zarge-zargen da aka kakaba masa ba gaskiya ba ne

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kogi, Nigeria - Sanatan Kogi ta Gabas, Jibrin Isah, da shugabannin APC na Odu ta 2 a ƙaramar hukumar Dekina ta jihar Kogi sun fara ka-ce-na-ce kan dakatar da shi daga jam’iyyar.

A cikin wata sanarwa mai ɗauke da ranar 26 ga watan Mayu, 2026, wadda aka aika wa shugaban APC na jihar a Lokoja, shugabannin mazabar sun dakatar da Sanata Jibrin Isah, wanda aka fi sani da Echocho.

Kara karanta wannan

Mai dokar barci: Sojoji sun damke 'dan bijilanti da zargin yi wa ISWAP leken asiri

Jibrin Isah.
Sanata mai wakiltar Kogi ta Gabas a Majalisar Dattawa, Jibrin Isah Hoto: Ganye 24
Source: Facebook

APC ta dakatar da sanata a Kogi

The Cable ta ruwaito cewa APC ta dakatar da sanatan ne bisa zarge-zargin da suka shafi cin mana da yi wa jam'iyya zagon kasa.

Shugabannin APC na mazabar Odu sun kuma yi zargin cewa sanatan ya kasa kawo nasara ga jam’iyyar a rumfar zaɓensa a zaɓukan gwamnan jihar Kogi na shekarun 2019 da 2023.

Dalilin dakatar da Sanata Jibrin

Sanarwar ta ce:

“Ya zo mana da takaici yadda Sanata mai wakiltar Kogi ta Gabas, Jibrin Isah (Echocho), ya daɗe yana aikata ayyukan adawa da jam’iyya."
“Sanatan ya kasa kawo nasara har a rumfar zaɓensa a zaɓukan gwamnan jihar Kogi na 2019 da 2023. Ya yi aiki da ya saɓa wa muradun jam’iyya a mazabarsa, ƙaramar hukumarsa da kuma yankin da yake wakilta.”

Shugabannin APC ɗin sun kuma zargi sanatan da gudanar da tarurruka da jam’iyyun adawa.

“Sanatan yana gudanar da jerin tarurruka da jam’iyyun adawa, abin da ya saɓa wa kundin tsarin APC kuma bai dace da matsayinsa a jam’iyyar ba,” in ji sanarwar.

Kara karanta wannan

Zaben fitar da gwani: Diyar Tinubu ta yi barazanar jagorantar zanga zanga a APC

“Saboda haka, APC ta mazabar Odu a ƙaramar hukumar Dekina ta jihar Kogi, bayan taron da ta yi a ranar 26 ga Mayu, 2027, ta amince da dakatar da Sanata Jibrin Isah (Echocho) daga APC,” in ji sanarwar.
Jam'iyyar APC.
Tutar jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya Hoto: @OfficialAPCNig
Source: Getty Images

Sanata Echocho ya yi watsi da dakatarwar

Sai dai mai magana da yawun sanatan, Mikail Ibrahim, ya yi watsi da dakatarwar, yana mai cewa ba ta da tushe ko inganci.

A wata sanarwa da ya fitar domin mayar da martani, Ibrahim ya ce Sanata Echocho ya yi nasara a rumfar zaɓensa tare da bayar da gagarumar gudunmawa ga nasarar APC a zaɓukan 2019 da 2023.

A wani labarin, kun ji cewa

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262