Ma'aikatan Gwamnatin Tarayya Sun Yi Watsi da Tayin N100,000 a Matsayin Mafi Karancin Albashi

Ma'aikatan Gwamnatin Tarayya Sun Yi Watsi da Tayin N100,000 a Matsayin Mafi Karancin Albashi

  • Ana ci gaba da sukar tayin gwamnonin Najeriya na kara mafi karancin albashin ma'aikatan gwamnati daga N70,000 zuwa N100,000
  • Kungiyar ma'aikatan gwamnatin tarayya (FWF) ta yi watsi da tayin gwamnonin, tana mai cewa adadin bai dace da halin da ma'aikata ke ciki ba
  • FWF ta kuma bai wa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu wa'adin wata guda ya magance duk wani nau'in matsalar tsaro

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Kungiyar ma'aikatan gwamnatin tarayya (FWF) ta yi watsi da shirin karin mafi karancin albashi zuwa N100,000.

Kungiyar ta bayyana cewa adadin bai dace da halin matsin rayuwa da ma’aikatan Najeriya ke ciki ba.

Shugaba Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnatin Najeriya Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa kungiyar FWF ta bayyana hakan ne a wani taro na jin ra’ayi da ta gudanar kan matsalolin tsadar rayuwa da rashin tsaro a fadin kasar nan.

Kara karanta wannan

Maganar gwamnan Kwara ta tsokano kungiyar kwadago kan mafi karancin albashi a Najeriya

Halin da ma'aikatan gwamnati ke ciki

A cewarta, ma’aikatan gwamnatin tarayya na fama da karancin albashi, bashin hakkoki da gwamnati ta ki biyansu da kuma tabarbarewar tsaro.

FWF ta ce aiwatar da mafi karancin albashin N70,000 bai kawo saukin da ake tsammani ba, domin bai warware matsaloli sa dawainiyar ma’aikata ba.

Ta kuma yi zargin cewa karin albashin da aka yi bai wadatar ba, yayin da wasu hakkoki da gwamnati ta yi alkawarin biya har yanzu ba a biya su ba.

FWF ta yi fatali da tayin N100,000

Kungiyar ta soki shawarar karin albashi zuwa N100,000 da wasu gwamnoni ke goyon baya, tana mai cewa adadin ba zai iya zama albashin da zai wadatar da ma’aikaci ba a halin da tattalin arzikin kasar ke ciki.

“Muna yin Allah wadai da wannan shawara kuma muna watsi da ita baki daya,” in ji kungiyar FWF.

FWF ta bayyana cewa hauhawar farashin kayayyaki, tsadar man fetur, faduwar darajar Naira da karin kudin wutar lantarki sun kara jefa ma’aikata cikin mawuyacin hali.

Kara karanta wannan

Gwamnoni sun bukaci Tinubu ya dawo da mafi karancin albashi N100,000

Haka kuma kungiyar ta nuna damuwa kan matsalar rashin tsaro, tana mai cewa ma’aikata da sauran ‘yan kasa na ci gaba da fadawa hannun masu garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka.

Kungiyar ta bukaci Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) da TUC su ayyana yajin aiki na sai baba-ta-gani domin matsa wa gwamnati lamba ta magance matsalolin da ake fuskanta.

Takardun kudi.
Takardun halastattun kudin da ake amfani da su a Najeriya Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Kungiyar FWF ta ba Tinubu wa'adin wata 1

FWF ta kuma bukaci gwamnatin tarayya da ta biya dukkan basussukan hakkokin ma’aikata tare da kirkiro alawus na tsadar rayuwa domin rage radadin halin da ake ciki, cewar rahoton Punch.

A karshe, kungiyar ta bai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu wa’adin kwanaki 30 da ya dauki matakan gaggawa wajen magance matsalar rashin tsaro, kashe-kashe, garkuwa da mutane da kuma tsadar rayuwa.

NLC ta bukaci a fara biyan ma'aikata N1m

A baya, kun ji cewa kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi fatali da yunkurin gwamnoni na kara mafi karancin albashin ma'aikata zuwa N100,000.

NLC ta ce idan aka yi la'akari da hauhawar farashi, ƙarin kuɗin wutar lantarki da tsadar man fetur, ma'aikata sun cancanci a biya albashin Naira miliyan 1 mafi karanci.

Ta yi nuni da cewa kuɗaɗen shiga da gwamnatoci ke samu a yanzu sun karu idan aka kwatanta da shekarun baya, don haka babu wani dalili da zai hana inganta walwalar ma’aikata.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262