Farashin Kosasshen Rago Ya Haura N700,000 ana Shirin Babbar Sallah a Jihar Kano

Farashin Kosasshen Rago Ya Haura N700,000 ana Shirin Babbar Sallah a Jihar Kano

  • Yan kasuwar dabbobi sun nuna damuwa kan karancin cinikin raguna yayin da babbar Sallah ke kara gabatowa a jihar Kano
  • Bincike ya nuna cewa a wasu kasuwannin dabbobi a Kano, ana sayar da kanana, matsakaita da manyan raguna tsakanin N150,000-N700,000
  • Shugaban ƙungiyar dillalan dabbobi ta jihar Kano, Bashir Sule-Dantsoho, ya koka kan karancin ciniki duk da yawan ragunan da aka kawo

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Masu sayar da raguna a kasuwannin dabbobi na Jihar Kano sun bayyana damuwa kan ƙarancin ciniki duk da cewa farashin raguna ya kai tsakanin N150,000 zuwa N700,000.

Hakan na zuwa ne ƙasa da mako guda gabanin fara bukukuwan Eid-el-Kabir, da aka fi sani da sallar layya ko babbar Sallah, ibadar da ta samo asali daga tarihin Annabi Ibrahim (AS).

Kara karanta wannan

Rigima ta barke bayan zaben fitar da gwanin APC, an kashe mutum 1 a jihar Kaduna

Raguna.
Wasu raguna a kasuwar dabbobi a jihar Kaduna Hoto: Bello Ado Mohammed
Source: Facebook

Daily Trust ta ce ana gudanar da wannan ibada ne a ranar 10 ga watan Zul Hijjah, wata na 12 a kalandar Musulunci, ga Musulman da ba su je aikin Hajji ba.

Farashin raguna a jihar Kano

Wani bincike da aka gudanar a kasuwannin dabbobi na Goron Dutse da Kofar Na’isa a cikin birnin Kano ya nuna cewa ‘yan kasuwa sun tanadi dabbobi masu yawa saboda gabatowar babbar Sallah.

A kasuwar Goron Dutse, shugaban ƙungiyar dillalan dabbobi ta jihar Kano, Bashir Sule-Dantsoho, ya ce duk da yawan dabbobin da ake da su, har yanzu babu ciniki sosai saboda matsin tattalin arziki.

Ya ce ƙananan raguna yanzu ana sayar da su tsakanin N150,000 zuwa N200,000, matsakaita kuma tsakanin N350,000 zuwa N500,000, yayin da manyan raguna ke kaiwa N700,000 ko fiye da haka.

A cewarsa, farashin raƙuma yanzu ya kai daga N500,000 zuwa Naira miliyan 3, yayin da bijimai da shanu ke tsakanin N600,000 zuwa Naira miliyan 3 gwargwadon girma da inganci.

Kara karanta wannan

"Ku tashi tsaye ku kare kan ku daga ƴan bindiga," Hadimin Tinubu ga ƴan Najeriya

Dalilin tashin farashin dabbobi a Kano

Sule-Dantsoho ya bayyana cewa tashin farashin ya samo asali ne daga tsadar abincin dabbobi da kuma kuɗin sufuri daga wuraren kiwo na ciki da wajen jihar.

Ya ce:

“Bara buhun abincin dabbobi ana sayar da shi tsakanin N10,000 zuwa N13,000, amma yanzu ya kai kusan N25,000.
Kano.
Taswirar jihar Kano da ke Arewa maso Yammacin Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Yan kasuwa sun ce ba a cinikin raguna

Haka kuma a kasuwar Kofar Na’isa, wani dillalin dabbobi mai suna Kabiru Mustapha ya danganta ƙarancin masu saye da halin ƙuncin rayuwa da ake ciki a ƙasar.

Ya ce farashin raƙuma a kasuwar yana tsakanin N500,000 zuwa Naira miliyan 2.5, yayin da shanu ke tsakanin N400,000 zuwa Naira miliyan 3.

A cewarsa, ƙananan raguna suna farawa daga N150,000, yayin da matsakaita da manya ke kaiwa sama da N550,000, kamar yadda The Nation ta kawo.

Ya ƙara da cewa mutane da dama sun fi son jiran kwanaki kaɗan kafin sallah ko ma ranar sallah domin ganin ko farashin zai sauka.

Kara karanta wannan

Yadda aka ci zarafin Musulmi kan radin suna a Najeriya, kungiya ta yi korafi

Raguna aun yi tsada a Kaduna

A wani labarin, kun ji cewa farashin raguna ya yi tashin gwauron zabi a wsu kasuwannin jihar Kaduna yayin da musulmi ke shirye-shiryen sallar layya.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya sa mutane da dama sun dakatar da sayen dabbar da za su yi layya da ita duk da wadatar dabbobin a kasuwanni.

Wani dillalin dabbobi a kasuwar Rigasa, Alhaji Suleiman Adamu, ya danganta tashin farashin da tsadar sufuri, abincin dabbobi da kuma matsalar tsaro

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262