Eid El Adha: Sarkin Musulmi Ya Fadi Ranar da Za a Yi Babbar Sallah a Najeriya

Eid El Adha: Sarkin Musulmi Ya Fadi Ranar da Za a Yi Babbar Sallah a Najeriya

  • Fadar Sarkin Musulmi ta tabbatar da cewa an ga jinjirin watan Dhul Hijjah, wanda ke nuna cewa watan Dhul Qa'adah ya kare a ranar Lahadi
  • Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar II ya ayyana Litinin, 18 ga watan Mayu a matsayin 1 ga watan Dhul Hijjah, 1447H
  • Hakan dai na nufin musulmin Najeriya za su yi hawan idin sallar layya a makon gobe, ranar Laraba, 27 ga watan Mayun, 2026

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Sokoto - Mai alfarma sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III ya sanar da cewa an ga jinjirin watan Dhul Hijjah a ranar Lahadi, 17 ga watan Mayu, 2026 a Najeriya.

Sultan ya bayyana ranar Litinin, 18 ga watan Mayu, 2026 a matsayin 1 ga watan Dhul Hijjah na shekarar 1447H, watan sallar layya.

Kara karanta wannan

Bayan ganin jinjirin wata, Saudiyya ta sanar da ranakun hawan Arafah da babbar Sallah

An sanar da ganin jinjirin watan Dhul Hijjah a Najeriya
Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III ya ce an ga jaririn watan Dhul Hijjah a Najeriya Hoto: Daular Usmaniyya, Getty Images
Source: Getty Images

An samu labarin ganin wata a Najeriya

Wani dan kwamitin ganin wata na fadar sarkin musulmi kuma masanin ilimin taurari, Simwal Usman Jibrin ne ya bayyana hakan a shafinsa na Facebook.

Simwal ya ce:

"Assalamu alaikum, Mai Alfarma Sarkin Musulmi na Sakkwato ya bayyana gobe Litinin, 18 ga Mayu, a matsayin ranar farko ta watan Dhul Hijjah.
"Nan ba da jimawa ba fadar sarkin musulmi za ta fitar da cikakken bayani a hukumance in sha Allah."

Hakan dai na nuna cewa al'ummar musulmi a Najeriya za su yi babbar sallah watau 'Eid El Adha' a ranar Laraba, 27 ga watan Mayu, 2026, daidai da 10 ga watan Dhul Hijjah, 1447.

Sallah: Sanarwa daga fadar sarkin Musulmi

Jim kadan kuwa, fadar Sarkin Musulmi ta fitar da sanarwa a hukumance, tana mai tabbatar da ganin jaririn watan Dhul Hijjah a Najeriya, kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito.

Sanarwar na ɗauke da sa hannun shugaban kwamitin kula da harkokin addinai na fadar Sarkin Musulmi, Farfesa Sambo Wali Junaidu.

Kara karanta wannan

Allah ya kawo mu, Sarkin Musulmi ya fitar da sanarwa kan ranar babbar Sallah a Najeriya

Ya ce mai alfarma Sarkin Musulmi wanda shi ne shugaban Majalisar ƙoli mai kula da harkokin musulunci a Najeriya (NSCIA), Alhaji Sa'ad Abubakar ya ayyana Litinin a matsayin 1 ga Dhul Hijjah.

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III ya sanar da ganin watan babbar sallah a Najeriya.
Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III a wajen taro. Hoto: Daular Usmaniyya
Source: Facebook

Farfesa Sambo Wali ya ce:

"Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar, CFR, mni, shugaban Majalisar kula da harkokin musulunci (NSCIA) ya bayyana Litinin a matsayin ranar farko a watan Dhul Hijjah.

Wannan wata na Dhul Hijjah na da matuƙar daraja a addinin musulunci, a cikinsa ne musulmi ke yin ibadar aikin hajji, ɗaya daga cikin rukunan addinin.

An ga watan sallar layya a Saudiyya

A wani labarin, kun ji cewa hukumomin Saudiyya sun bayyana cewa an ga jinjirin watan Dhul Hijjah a ranar Talata, 29 ga watan Dhul Qa'adah, 1447 daidai da 17 ga watan Mayu.

A cewar sanarwar da mahukuntan Saudiyya suka fitar, alhazai za su yi hawan Arafah a ranar Talata, 9 ga watan Dhul Hijjah, wanda zai yi daidai da 26 ga watan Yuni, 2026.

Wannan sanarwa dai ta tabbatar da cewa watan Dhul Qa'adah ya kare, yau Litinin ne 1 ga watan Dhul Hijjah, 1447H, sannan ranar Laraba, 27 ga Mayu za a yi sallah.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com