Trump Ya Ja da Baya kan Kai Munanan Hare Hare kan Iran, an Ji Dalili
- Shugaba Donald Trump ya ce ya janye shirin kai hari kan Iran muddin za a iya cimma yarjejeniya cikin gaggawa
- Donald Trump ya ce Iran da wasu kasashen Gabas ta Tsakiya sun bukaci Amurka ta dakatar da kai harin
- Rahotanni sun ce Yariman Saudiyya, Mohammed bin Salman, ya nuna damuwa kan shirin kara kai hare-hare kan Iran
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Birnin Washington, Amurka - Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce ya janye shirin kai hari kan Iran bisa sharadin cewa za a iya cimma yarjejeniya cikin gaggawa.
Trump ya ce Iran da wasu kasashen Gabas ta Tsakiya sun bukaci Amurka ta dakatar da kai hare-hare, yana mai cewa an riga an cimma matsaya kan muhimman sharuddan yarjejeniyar.

Source: Twitter
Shugaba Trump ya bayyana hakan ne a wani rubutu da ya yi a shafinsa na Truth Social a ranar Lahadi, 2 ga watan Agustan 2026.
Ya ce yarjejeniyar za ta hada da bude mashigar Hormuz baki daya cikin gaggawa tare da kawo karshen barazanar shirin nukiliyar Iran.
Trump ya bayyana matsayar Amurka
Trump ya ce Amurka ta shirya tsaf domin daukar matakin soji kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran da karfin da ba a gani ba tun bayan yakin duniya na biyu.
“Amurka ta shirya tsaf kuma tana cikin shirin kai hari kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran da matakin karfin soja da iko da ba a taba gani ba tun bayan yakin duniya na biyu.”
- Shugaba Donald Trump
Trump ya ce duk da wannan shiri, Iran da wasu kasashen Gabas ta Tsakiya sun bukaci a dakatar da kai harin saboda an amince da muhimman sharuddan yarjejeniya.
Ya kara da cewa:
“Wannan zai hada da bude mashigar Hormuz cikin gaggawa, baki daya kuma ba tare da wani sharadi ba, tare da kawo karshen barazanar nukiliyar Iran.”
Trump ya janye shirin kai hari
Trump ya ce ya amince da janye harin domin amfanin duniya da kuma tabbatar da makomar Iran mai nasara da wadata.
“Bisa wannan bukata, na amince da janye harin domin amfanin duniya a nan gaba, tare da tabbatar da ci gaban Iran mai nasara da wadata, bisa sharadin cewa za a iya cimma yarjejeniya cikin gaggawa.”
Shugaban Amurka ya ce kasar Isra’ila ma ta amince da wannan matsaya.
“Kowa ya fara aiki, a tabbatar an kammala yarjejeniyar.”
- Shugaba Donald Trump

Source: Getty Images
Yariman Saudiyya ya yi magana
Rahotannin kafafen yada labarai na Amurka sun ce Yariman Saudiyya, Mohammed bin Salman, ya tattauna da Trump ta waya a ranar Asabar.
Rahotannin Axios da kamfanin dillancin labarai na Associated Press (AP) sun ce yariman ya nuna damuwa kan shirin kara kai hare-hare kan Iran.
Axios, yana mai nakalto wani jami’in Amurka, ya ce Yarima Mohammed ya bayyana damuwarsa tare da neman karin bayani kan shirin daukar matakin.
Wata majiya da ke da masaniya kan lamarin ta ce yariman ya bukaci Trump ya rage tashin hankali tare da kauce wa kaddamar da hare-haren.
Iran ta lalata jiragen yakin Amurka
A wani labarin kuma, kun ji cewa rundunar kare juyin juya halin Musulunci ta Iran (IRGC) ta yi ikirarin lalata jiragen yaƙin F-35 guda uku na Amurka.
Rundunar IRGC ta kuma bayyana cewa ta yi wa wasu jiragen guda uku mummunar ɓarna a wani hari da ta kai sansanin sojojin sama na al-Azraq da ke kasar Jordan.
Asali: Legit.ng


