Matatar Dangote Ta Yi Rangwame a Farashin Litar Man Jiragen Sama a Najeriya

Matatar Dangote Ta Yi Rangwame a Farashin Litar Man Jiragen Sama a Najeriya

  • Matatar Dangote ta rage farashin kowace litar man jiragen sama na Jet A1 daga N1,750 zuwa N1,650 a Najeriya
  • Wannan rangwame na zuwa ne yayin da kamfanonin jiragen sama auna fara kokawa kan tsadar mai tare da barazanar dakatar da ayyukansu
  • Ana sa ran rage farashin zai taimaka wajen saukaka kudin sayen mai ga kamfanonin jiragen sama tare da daidaita harkokin zirga-zirga

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Lagos, Nigeria - Matatar Dangote da ke jihar Legas ta rage farashin man jiragen sama na Jet A1 daga N1,750 zuwa N1,650 kan kowace lita.

Matatar hamshakin attajirin, wanda ya fi kowa arziki a nahiyar Afirka ta yi haka ne domin rage wa kamfanonin jiragen sama nauyin kashe kudade tare da tabbatar da wadataccen mai a fadin kasa.

Dangote.
Attajirin dan kasuwa kuma shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote da rumbun ajiyar mai Hoto: @Dangotegroup
Source: UGC

Dangote ya rage farashin man jirgi

Kara karanta wannan

Bidiyo: Yadda jiragen yakin Amurka suka yi karo da juna a sama, suka tarwatse

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da matatar ta fitar ranar Litinin, 18 ga watan Mayu, 2026, kamar yadda jaridar Tribune Nigeria ta ruwaito

Matatar ta ce ta kuma samar da damar bashi na kwanaki 30 ba tare da ruwa ba ga ‘yan kasuwa da kamfanonin jiragen sama, tare da kariyar garantin banki.

Haka zalika, ta kuma sanar da sauya tsarin sayar da man daga farashin Dala zuwa tsarin farashin Naira.

Kamfanonin jirage na fuskantar matsi

Wannan mataki na zuwa ne yayin da kamfanonin jiragen sama na cikin gida ke fama da tsadar gudanar da aiki, inda farashin man jiragen sama ke cin kaso mai yawa na kudaden su.

Masu ruwa da tsaki a bangaren sufurin jiragen sama sun dade suna nuna damuwa kan tashin farashin Jet A1, suna gargadin cewa hakan na jefa kamfanonin cikin matsin tattali tare da barazana ga ci gaba da zirga-zirgar jirage a Najeriya.

Ana sa ran rage farashin zai taimaka wajen saukaka kudin sayen mai ga kamfanonin jiragen sama, daidaita harkokin zirga-zirga tare da rage tsadar kudin tikitin jirage ga fasinjoji.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga: Matasa sun yi bore a Kano, sun kona wani ginin gwamnati

Dangote zai sayar wa mutane hannun jari

Wannan na zuwa ne kwanaki kadan bayan shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, ya bayyana cewa kamfanin ya ki amincewa da yunkurin NNPCl na kara sayen hannun jari a matatar fiye da kaso 7.25 cikin 100 da take da shi yanzu.

Jiragen sama.
Jirgin sama yayin da yake kan hanya a sararin samaniya Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Ya ce an dauki matakin ne domin bai wa talakawan Najeriya damar mallakar hannun jari a matatar maimakon takaita shi ga wasu tsirarun masu zuba jari.

“Idan ka dubi matatar mu, kamfanin mai na kasa ya riga ya mallaki kaso 7.25 cikin 100 kuma suna kokarin kara saye amma mu muka ce a’a, muna son sauran jama'a su samu damar zama wani bangare na matatar,” in ji Dangote.

Matatar Dangote ta rage farashin fetur

A wani rahoton, kun ji cewa matatar Dangote ta janye ƙarin farashin fetur da ta yi a baya, inda ta mayar da farashin kowace lita na fetur zuwa N1,275.

Kara karanta wannan

'Yan kasuwa sun kara farashin buhun siminti a Najeriya, yanzu ya haura N12,500

Wani babban jami’i a matatar man Dangote, wanda ya buƙaci a sakaya sunansa, ya tabbatar da ƙarin farashin na farko amma ya ce matatar yanzu ta janye shi.

Ya bayyana cewa an ɗauki wannan shawarar cikin gaggawa ne sakamakon sauyin da aka samu, musamman faɗuwar farashin ɗanyen mai a kasuwannin duniya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262