Abu Mainok: Tinubu Ya Yi Magana kan Kwamandan ISIS da Sojojin Amurka Suka Kashe a Najeriya
Abuja, Nigeria - Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da kashe wani babban kwamandan ƙungiyar ta'addanci (ISIS) mai suna Abu-Bilal Al-Manuki, wanda aka fi sani da Abu-Mainok a Najeriya.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
An kaahe kasurgumin dan ta'addan ne a wani samame na haɗin gwiwa tsakanin sojojin Najeriya da na Amurka a yankin Tafkin Chadi.

Source: Twitter
Tinubu ya tabbatar da halaka Abu Mainok ne a wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya wallafa a shafinsa na X.
Shugaba Tinubu ya bayyana aikin a matsayin babbar nasara a yaƙin da ake yi da ta’addanci tare da misali mai ƙarfi na haɗin gwiwar tsaro tsakanin Najeriya da Amurka.
A cewar shugaban ƙasar, rundunar sojojin Najeriya tare da haɗin gwiwar sojojin Amurka sun kai samamen cikin dare, inda suka kashe Al-Manuki tare da wasu manyan kwamandojinsa a yankin Tafkin Chadi.
Tinubu ya ce samamen ya yi wa ƙungiyar ISIS mummunar illa tare da sake tabbatar da aniyar Najeriya na ci gaba da matsa lamba kan ƙungiyoyin ta’addanci da ke aiki a ciki da wajen ƙasar.
“Jajirtattun sojojin Najeriya tare da haɗin gwiwar sojojin Amurka sun gudanar da wani gagarumin samame wanda ya yi wa ƙungiyar ISIS mummunar illa."
“Rahotannin farko sun tabbatar da kashe babban jagoran ISIS da ake nema ruwa a jallo, Abu-Bilal Al-Manuki wanda aka fi sani da Abu-Mainok, tare da wasu daga cikin manyan kwamandojinsa.”
- In ji Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Shugaban ya gode wa Amurka saboda haɗin gwiwar da take bayarwa wajen cimma manufofin tsaro na bai ɗaya, tare da nuna godiyarsa ga shugaban Amurka Donald Trump bisa jagoranci da goyon bayan da yake bayarwa.
“Najeriya na matuƙar yaba da wannan haɗin gwiwa da Amurka wajen bunƙasa manufofin tsaro na bai ɗaya. Ina miƙa godiyata ga Shugaba Trump saboda jagoranci da goyon bayan da yake bayarwa a wannan yunƙuri,” in ji Tinubu.
Ya kuma yabawa jami’an sojin ƙasashen biyu bisa ƙwarewa da jarumtakar da suka nuna yayin gudanar da samamen, yana mai bayyana fatan cewa za a ci gaba da kai irin waɗannan hare-hare masu ƙarfi kan sansanonin ‘yan ta’adda.
Asali: Legit.ng
