Kamfanin Rano Air Ya Dakatar da Sufurin Jiragensa zuwa Wasu Jihohi a Najeriya

Kamfanin Rano Air Ya Dakatar da Sufurin Jiragensa zuwa Wasu Jihohi a Najeriya

  • Kamfanin sufuri na Rano Air ya nuna damuwa kan tsadar man jirgin sama, wanda ya tashi da sama da 300% a Najeriya
  • Sakamakon haka ne kamfanin ya sanar da dakatar da zirga-zirgan jiragensa a wasu hanyoyi na 'dan takaitaccen lokacin saboda tsadar mai
  • Duk da bai bayyana hanyoyin da zai dakatar da aiki na, wata majiya ta ce Maiduguri da Gombe na cikin wadanda matakin zai shafa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Kamfanin jiragen sama na Rano Air ya sanar da dakatar da wasu daga cikin hanyoyin zirga-zirgarsa na wucin gadi bayan tashin farashin man jiragi na Jet A1 da sama da 300%.

Ya ce hauhawar farashin man jiragen sama ya sa gudanar da sufurin jiragen sama zuwa wasu jihohi ya zama mai matuƙar wahala da rashin riba.

Kara karanta wannan

Sabon rikici ya barke a garuruwan jihar Kogi, an rasa rayukan mutane masu yawa

Rano Air.
Jirgin sama na kamfanin sufurin Rano Air da ke aiki a wasu jihohin Najeirya Hoto: Rano Air
Source: UGC

Rano Air ya dakatar da aiki a wasu hanyoyi

Kamfanin ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, wanda aka fi sani da Twitter yau Juma'a.

Sai dai kamfanin Rano Air bai fayyace wadanne jihohi ne zai dakatar sufurin jiragensa ba a cikin sanarwar.

Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa manema labarai cewa hanyoyin Maiduguri da Gombe na daga cikin waɗanda ake tunanin za a dakatar na ɗan lokaci.

A halin yanzu, Rano Air na zirga-zirga tsakanin Abuja, Legas, Kano, Sakkwato, Maiduguri, Kaduna, Katsina, Bauchi da Osubi.

Majiyar ta ce:

“Tabbas za a iya dakatar da sufuri a sama da rabin hanyoyin da kamfanin ?$ gudanar da ayyukansa, amma nan ba da jimawa ba mahukunta za su fitar da cikakken bayani.”

Dalilin Rano Air na daukar mataki

A cikin sanarwar, kamfanin ya ce tashin farashin man jiragen ya jefa harkokin sufuri cikin matsin lamba mai tsanani, lamarin da ya tilasta musu ɗaukar matakin dakatar da wasu hanyoyi.

Kara karanta wannan

Kano da wasu jihohin Arewa 11 za su fuskanci tsananin zafi, NiMet ta yi gargadi

Kamfanin ya nuna damuwa kan matsalolin da hakan zai iya jawo wa fasinjoji da abokan hulɗarsa, yana mai cewa an ɗauki matakin ne bayan dogon nazari domin tabbatar da tsaro, inganci da dorewar ayyuka.

Rano Air zai maida wa fasinjoji kudinsu

Rano Air ya kuma tabbatar wa da fasinjojin da suka riga suka zayi tikitin tafiya cewa za a taimaka musu wajen mayar da kuɗi, sauya lokaci ko canza hanyar tafiya.

Kamfanin ya ƙara da cewa zai dawo da zirga-zirga a hanyoyin da aka dakatar da zarar yanayi ya daidaita kuma harkokin suka koma yadda za su kasance masu anfani.

Jirgin sama
Jirgin sama a lokacin da yake taakiyar tafiya a sararin samaniya Hoto: Anadolu
Source: Getty Images

Daily Trust ta ruwaito cewa kamfanonin jiragen sama na cikin gida sun dade suna kokawa kan tsadar man jiragen sama, har ma wasu suka yi barazanar dakatar da aiki gaba ɗaya.

Ko da yake gwamnatin tarayya ta shiga tsakani domin dakile hakan, wasu daga cikin kamfanonin sun ce har yanzu suna sayen mai kusan Naira 3,000 kan kowace lita.

An bullo da shirin lamunin hawa jirgi

A wani labarin, kun ji cewa Gwamnatin Najeriya ta bullo da wani shiri na ba da lamunin sayen tikitin jirgin sama domin saukakawa mutane zirga-zirga.

Kara karanta wannan

Daga rantsar da mataimakin gwamna, 'yan daba sun hallaka matasa 5 a Kano

Gwamnatin ta ƙaddamar da sabon tsarin mai suna “Fly Now, Pay Later” domin bai wa ‘yan Najeriya damar yin tafiye-tafiyen jirgin sama cikin sauƙi.

Ta ce an samar da wannan tsari ne domin rage nauyin biyan kuɗin tikiti gaba ɗaya, wanda sau da yawa ke hana mutane yin tafiya a jiragen sama domin biyan bukatunsu a kan lokaci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262