Gwamnatin Tinubu Za Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.1 a Kaduna, Uba Sani Ya Yi Bayani

Gwamnatin Tinubu Za Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.1 a Kaduna, Uba Sani Ya Yi Bayani

  • Gwamnatin Tarayya ta amince da manyan kwangiloli guda biyu na ayyukan more rayuwa a jihar Kaduna waɗanda darajarsu ta haura Naira triliyan ɗaya
  • Ayyukan sun haɗa da ginin layin dogo na zamani da kuma gyaran babbar hanyar Mando zuwa Birnin Gwari
  • Gwamna Uba Sani ya jinjina wa Shugaba Bola Tinubu, inda ya bayyana tasirin wadannan ayyukan ga sauya fasalin tattalin arziki da sufuri a Kaduna

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Kaduna – Gwamnatin Tarayya ta amince da ware maƙudan kuɗaɗe domin aiwatar da manyan ayyukan raya ƙasa a jihar Kaduna, matakin da ake kallo a matsayin gagarumin ci gaba ga yankin Arewa maso Yamma.

Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (FEC) ce ta amince da waɗannan ayyuka waɗanda suka haɗa da gina layin dogo na cikin birni da kuma gyaran babbar hanyar da ta daɗe tana ci wa jama'a tuwo a ƙwarya.

Kara karanta wannan

Yunwa a Arewa: Tinubu ya ware tireloli 100 na abinci, makudan kudi ga jihohi 19

Uba Sani ya jinjinawa Tinubu da gwamnatin tarayya ta amince da kashe N1.1trn a Kaduna
Shugaba Bola Tinubu ya karbi bakuncin Gwamna Uba Sani a fadar shugaban kasa Abuja. Hoto: @ubasanius
Source: Twitter

Aikin layin dogo na cikin Kaduna

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ne ya bayyana hakan a cikin wani sakon godiya da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya yi bayani dalla dalla game da ayyukan da za a yi.

Da farko, Uba Sani ya tabo batun aikin layin dogo, wanda darajarsa ta kai kusan Naira triliyan ɗaya, zai mamaye tsawon kilomita 50 a cikin birnin Kaduna.

Layin dogon zai haɗa muhimman sassa na birnin kamar haka:

  • Kilomita 30: Daga Rigachikun zuwa Sabon Tasha.
  • Kilomita 20: Daga Millennium City zuwa Rigasa.

Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa wannan aiki zai sa Kaduna ta zama jiha ta biyu kacal a Najeriya da ke da irin wannan tsarin sufuri na zamani.

Aikin ya yi daidai da tsarin gyaran sufuri na jihar, wanda ya riga ya haɗa da ginin hanyar motocin safa na BRT mai tsawon kilomita 24.

Kara karanta wannan

Sanatan APC ya bijirewa gwamna, ya yi fatali da zabin wanda zai gaje shi a 2027

Gyaran hanyar mando zuwa Birnin Gwari

Aiki na biyu shi ne sake gina babbar hanyar Mando zuwa Birnin Gwari mai tsawon kilomita 122, akan kuɗi Naira biliyan 178.

Wannan hanya tana da matuƙar muhimmanci, inda za ta ta taimaka wa jami'an tsaro wajen gudanar da ayyukansu cikin sauri.

Hanyar za ta kuma sauƙaƙa jigilar kayan gona daga yankunan karkara yayin da za ta sake buɗe yankunan da suka daɗe a killace saboda rashin hanya.

Gwamna Sani ya tuna yadda Shugaba Tinubu ya ziyarci Birnin Gwari lokacin yaƙin neman zaɓe kuma ya yi alƙawarin gyara hanyar.

Uba Sani ya ce wadannan ayyuka da gwamnatin tarayya za ta aiwatar za su sauya tattalin arzikin Kaduna
Shugaba Bola Tinubu ya karbi bakuncin Gwamna Uba Sani a fadar shugaban kasa Abuja. Hoto: @ubasanius
Source: Facebook

Tasirin ayyukan ga tattalin arziki

Gwamnan ya tabbatar wa jama'ar jihar cewa gwamnatinsa za ta sanya ido sosai domin ganin an kammala waɗannan ayyuka cikin inganci.

A cewarsa, waɗannan ba ayyuka ba ne kawai na lokaci guda, a'a, jari ne na dogon lokaci da zai haɓaka tattalin arziƙin jihar da kuma sauƙaƙa rayuwar mazauna Kaduna.

Kara karanta wannan

Zargin kisan Kiristoci: Amurka za ta dauki mummunan mataki kan kasar Najeriya

Wannan mataki ya nuna kwarin gwiwar da Gwamnatin Tarayya ke da shi akan tsarin ci gaban jihar Kaduna da kuma iyawar gwamnatin jihar wajen aiwatar da manyan ayyuka.

Karanta sakon Uba Sani a nan kasa:

Kuri'un da Tinubu zai samu a Kaduna

A wani labari, mun ruwaito cewa, Gwamnan Kaduna, Uba Sani, ya yi magana game da kuri'un da Shugaba Bola Tinubu, zai samu a jihar a zaben 2027 da ake tunkara.

Gwamna Uba Sani ya nuna kwarin gwiwar cewa Shugaba Tinubu zai samu akalla kashi 70 cikin 100 na ƙuri’un jihar a lokacin babban zaɓen shekarar 2027.

Gwamna Uba Sani ya danganta hasashen nasa ga abin da ya bayyana a matsayin rawar gani da shugaban kasar yake takawa a kan mulki, wanda ya ce hakan ya gamsar da mutanen jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com