Labaran tattalin arzikin Najeriya
A labarin nan za a ji cewa bayan kalaman limamin Katolika, gwamnatin Bola Tinubu ta bayyana cewa za a rika aiki da tare da kungiyoyin addini domin a gyara kasa.
Hukumar SMEDAN ta sake bude shirin tallafin N50,000 ga kananan 'yan kasuwa ns kyauta, amma masu anfani dole ne su dauki akalla ma'aikaci daya aiki.
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce gwamnatin Abuja na shirin hana okada da adaidaita sahu a wasu sassan birnin saboda matsalar tsaro da rahotannin jami'an tsaro.
Kashim Shettima ya ce shugaba Bola Tinubu ya cancanci yabo ba suka ba kan sauye-sauyen tattalin arziki, yana mai cewa ajiyar kuɗin ƙasashen waje ta haura $52bn.
Gwamnatin Katsina za ta raba Naira biliyan 4 ga mazabu 361, inda kowace za ta samu Naira miliyan 10 domin gudanar da ayyukan ci gaba bayan amincewar Gwamna Radda.
A labarin nan, za a ji cewa gwamnatin tarayya ta mayar da martani ga zargin da Atiku Abubakar ya yi game da tattalin arziki da yadda ke tafiyar da shi.
Kamfanin NNPCL ya tura Naira tiriliyan 6.286 ga Asusun Tarayya cikin watanni shida na 2026, yayin da ayyukan manyan bututun iskar gas ke gab da kammalawa.
Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta haramta tsarin "attachment" ga direbobin adaidaita sahu, tare da umartar su su bi dokokin da ke inganta tsaro da ɗa’a.
Bankin EBID na ECOWAS ya bai wa gwamnatin jihar Bauchi rancen dala miliyan 91.63 domin gina tituna da gadoji 24, tare da samar da dubban guraben aiki.
Labaran tattalin arzikin Najeriya
Samu kari