Labaran tattalin arzikin Najeriya
Bankin Duniya ya toshe sashen sharhi a wasu bangarorin shafinsa na Instagram bayan yawaitar martani daga ’yan Najeriya biyo bayan rahoton sabon bashi ga Najeriya.
Farashin siminti ya kai N13,000 a Najeriya yayin da dillalai da masu gine-gine ke kokawa kan tsadar kaya da yawaitar karin farashi. Masana sun gargadi gwamnati.
Gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da shirin motocin CNG da lantarki a Kano domin rage kuɗin sufuri, bunƙasa makamashi mai tsafta da samar da ayyukan yi ga matasa.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya nuna damuwa kan tsarin hada-hadar kudin da duniya ke amfani da shi, ya ce yana durkusarda kasashen Afirka masu tasowa.
Ministocin Najeriya da Maroko sun tattauna kan aikin bututun iskar gas na NMGP a ranar 10 ga Mayu, 2026, inda ake sa ran Tinubu zai sanya hannu a ƙarshen shekara.
Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashin Shettima ya goyi bayan takarar Sanata Ahmed Aliyu Wadada a zaben gwamnan jihar Nasarawa a 2027 ya fadi haka ne a Nasarawa.
A labarin nan za a ji yadda dukiya fitaccen attajiran nan, Alhaji AbdulSamad Rabiu ta kara habaka a shekarar 2026 har ya kai ga kama babban kambu a Afrika.
Ministan kudi Taiwo Oyedele ya tabbatar da cewa gwamnatin Bola Tinubu ba za ta dawo da tallafin mai ba duk da koke-koken da ake yi kan tsadar fetur.
Gwamna Dikko Radda ya ƙaddamar da titin Ingawa–Dutsi–Shargalle mai tsawon 39km a Katsina domin bunƙasa kasuwanci da sauƙaƙa zirga-zirga a yankin.
Labaran tattalin arzikin Najeriya
Samu kari