Darma: Sabon Ministan da Tinubu Ya Nada Ya San Matsayarsa bayan Tantance Shi
- Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya rubuta wasika ga majalisar dattawa domin neman tantance Muttaqha Rabe Darma a matsayin Minista
- Majalisar dattawan ta tantance Muttaqha Rabe Darma yayin zamanta na ranar Alhamis, 23 ga watan Afirilun 2026
- A lokacin tantance shi, Muttaqha ya bayyana cewa zai yi aiki kafada da kafada da majalisar dokoki ta kasa don magance matsalar karancin gidaje
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Majalisar dattawa ta tantance Muttaqha Rabe Darma wanda ya fito daga jihar Katsina a matsayin Minista a tarayyar Najeriya.
Majalisar dattawan ta Najeriya ta tabbatar da Musttaqha Rabe Darma matsayin Minista bayan ta tantance shi da ta yi.

Source: Twitter
Jaridar Vanguard ta kawo rahoton cewa majalisar ta tabbatar da Muttaqha Rabe Darma ne a yayin zamanta na ranar Alhamis, 23 ga watan Afirilun 2026.

Kara karanta wannan
An fara tantance Muttaqa Darma a Majalisar Dattawa bayan Tinubu ya nada shi minista
Majalisa ta tabbatar da sabon Ministan Tinubu
Tabbatar da Darma ya biyo bayan zaman tantancewa ne, inda aka gudanar da tambayoyi da amsoshi.
Shugaba Bola Tinubu ya rubutawa majalisar dattawa wasiƙa a ranar Laraba, inda ya nemi a tantance tare da tabbatar da Muttaqha Rabe Darma a matsayin Minista.
Sanata Godswill Akpabio, wanda ya karanta saƙon daga Shugaba Tinubu, daga baya ya tura shi zuwa ga kwamitin da ke kula da hakan don ƙarin matakan majalisa, tare da umarnin ba da rahoto da zarar hakan ya yiwu.
Wane aiki sabon Ministan zai yi?
Muttaqha Rabe Darma, ya yi alƙawarin yin aiki kafaɗa da kafaɗa da majalisar dokoki ta kasa domin magance ƙarancin gidaje a Najeriya.
Ya bayyana tsare-tsare na inganta jagoranci, faɗaɗa hanyoyin samun gidaje masu sauƙin kuɗi, da kuma ƙarfafa ayyukan hukumomi a wannan ɓangaren, tashar Channels tv ta kawo rahoton.
Da yake magana yayin tantance shi a majalisar dattawa, Darma ya ce salonsa zai mayar da hankali ne kan dinke abin da ya siffanta da gibin jagoranci wanda ya kawo cikas ga samar da gidaje masu inganci a faɗin ƙasar.

Kara karanta wannan
Arewa da Kudu za su amfana da Tinubu ya nemi izinin sake ciyo bashin Dala miliyan 516
A cewarsa, haɗin gwiwa da ‘yan majalisa zai kasance mabuɗi wajen kawar da ƙalubalen da aka daɗe ana fuskanta a ɓangaren gidaje.
“Zamu yi aiki tare da majalisar dokoki ta kasa don tabbatar da cewa an magance ƙalubalen gidaje."
- Muttaqha Rabe Darma

Source: Facebook
Muttaqha Rabe Darma ya samo mafita
Ya lura cewa fiye da ‘yan Najeriya miliyan 100 ne matsalar ƙarancin gidaje ta shafa, sannan ya jaddada buƙatar sanya gidaje su kasance masu sauƙin samu da rahusa, musamman ga masu matsakaicin samun kuɗi.
Da yake mayar da martani ga damuwar da Sanata Adams Oshiomhole ya nuna, Darma ya yarda da girman ƙalubalen ƙarancin gidaje a Najeriya, amma ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa za a iya magance shi da ingantattun manufofi da jajircewa.
“Na yi amanna cewa komai mai yiwuwa ne. Zan yi duk abin da zan iya don dinke gibin da ke akwai tare da inganta yanayin."
- Muttaqha Rabe Darma
Tinubu ya mika bukata wajen majalisa
A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya mika sabuwar bukata ga majalisar dattawan Najeriya.

Kara karanta wannan
Sanatoci sun gana da Tinubu, an ruwaito cewa ya yi fatali da bukatarsu kan zaɓen 2027
Shugaba Tinubu ya nemi izinin majalisar dattawa domin sake ciyo bashin Dala miliyan 516.3 daga bankin Deutschk da ke kasar Jamus.
Mai girma Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta kinkimo wannan rancen ne domin gina babbar hanyar Sokoto zuwa Badagry.
Asali: Legit.ng