An Yi Rashin Babban Malamin Musulunci a Maiduguri, Sheikh Dazigau Tijjani
- Wani fitaccen malamin addinin Musulunci ya rasu a Maiduguri ranar Laraba, 5 ga Agusta, 2026 da muke ciki
- Wani matashi, Ibn Maigana ya sanar da rasuwar malamin, yana bayyana shi a matsayin mashahurin malami da ya ilmantar tare da tasiri ga al'ummar Bolori
- Bayan rasuwarsa, jama'a sun ci gaba da yi masa addu'a, yayin da aka tuna gudummawarsa ga addini, ilimi da tarbiyyar al'umma a Maiduguri da kewaye
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Maiduguri, Borno - Fitaccen malamin addinin Musulunci, Mallam Haruna Dazigau Tijjani, ya riga mu gidan gaskiya.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa an riga an yi jana'izarsa ranar Laraba, 5 ga Agusta, 2026, a unguwar Bolori da ke Maiduguri.

Source: Original
Wani daga cikin ƴaƴan abokin marigayin, Ibn Maigana, ne ya sanar da rasuwar malamin ta shafinsa na Facebook, inda ya bayyana shi a matsayin malami mai girma.
Ya ce marigayin ya koyar da mutane da dama, kuma darussansa sun yi tasiri sosai ga al'ummar Bolori da sauran mazauna Maiduguri.
An gudanar da jana'izarsa da misalin karfe hudu na yamma a gidansa da ke titin Goni Tijjani a Bolori, bisa koyarwar addinin Musulunci.
Ibn Maigana ya bayyana cewa marigayin yana da kyakkyawar alaka ta dangi da mahaifinsa, lamarin da ya sa rasuwar ta kasance abin jimami gare shi.
A cikin sakonsa ya rubuta cewa:
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un! Wannan sanarwa ce ta rasuwar Malam Haruna Tijjani Dazigau, fitaccen malamin addini a Bolori wanda ya koyar da yawancinmu ta hanyoyi daban-daban."
"An tsara jana'izarsa da karfe 4:00 na yamma a gidansa da ke Bolori, Maiduguri, a kan titin Goni Tijjani."
"Kafin rasuwarsa, Malam ya kasance dan uwa kuma aminin mahaifina. Allah Ya jikansa da rahama."
Maigana ya bukaci al'umma su ci gaba da yi wa marigayin addu'ar samun rahamar Allah, yana mai cewa tasirin da ya bari ya zarce iyakar karatun addini.
Asali: Legit.ng
