Wata Sabuwa: An Samu Sabani tsakanin Najeriya da Amurka kan Wasu Na'urori da Aka Kwato

Wata Sabuwa: An Samu Sabani tsakanin Najeriya da Amurka kan Wasu Na'urori da Aka Kwato

  • Dakarun Sojojin Najeriya sun saba wa ikirarin Amurka cewa ta kwace wasu muhimman kayayyaki daga ‘yan ta’adda
  • Hedikwatar tsaro ta ce gwamnatin Najeriya ce ta miƙa kayayyakin ga Amurka a wani bangare na aikin haɗin gwiwar tsaro
  • Amurka dai ta yi ikirarin cewa ta kashe mayaƙan jihadi 199 a wani samame da ta kawo Najeriya tare da kwato wasu muhimman kayayyaki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Mai magana da yawun rundunar sojin Najeriya ya saba wa kirarin babban jami’in gwamnatin Amurka cewa dakarun ƙasar sun ƙwace tarin na’urorin tara bayanan sirri daga hannun ‘yan ta’adda a Najeriya.

Tun farko Amurka ta yi ikirarin cewa sojojinta ne suka kwace kayan daga hannun yan ta'adda, sannan suka fice da su daga Najeriya.

Trump.
Shugaban Amurka, Donald Trump da takwaransa na Najeriya, Bola Ahmed Tinubu Hoto: @RealDonaldTrump, @aonanuga1956
Source: Twitter

Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro, Birgediya Janar Samaila Uba, ya shaida wa Premium Times cewa ba Amurka ce ta ƙwace na'urorin daga hannun ‘yan ta’adda ba.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Zamfara ta fara daukar sababbin ma'aikata, matasa 3050 za su samu aiki

Najeriya ta saba wa ikirarin Amurka

A cewarsa, gwamnatin Najeriya ce ta miƙa waɗannan kayayyaki ga Amurka a matsayin wani ɓangare na haɗin gwiwar yaƙi da ta’addanci tsakanin ƙasashen biyu.

Ya ce:

"Mu ne muka ba su kayayyakin. Wannan wani ɓangare ne na haɗin gwiwar tsaro tsakanin Najeriya da Amurka."

Wannan ne karo na farko da wani jami’in Najeriya ya yi bayani kan lamarin tun bayan da Amurka ta fara bayyana hakan.

Abin da jami'in Amurka ya faɗa

A ƙarshen watan Yuni, 2026, Mataimakin Mai Ba Shugaban Amurka Shawara kan Yaƙi da Ta’addanci, Sebastian Gorka, ya ce dakarun Amurka sun kwato na'urori masu tarin yawa daga ‘yan ta’adda a Najeriya.

Ya ce:

"Na ga yadda jami’anmu suka kashe mayaƙan jihadi 199 a hari guda, sannan muka kwato kayayyakinnsu da yawa."

Ya ƙara da cewa adadin kayayyakin da aka kwato ya hura nunki uku na duk wani irin abin da Amurka ta taɓa kwatowa daga abokan gaba tun bayan harin 11 ga Satumba, 2001.

Kara karanta wannan

Kasar musulunci ta Iran ba za ta miƙa wuya ba, ta shirya komawa yaƙi da Amurka

Hare-haren da Amurka ta kawo Najeriya

Ko da yake Gorka bai ambaci sunan farmakin ba, bayanansa sun yi daidai da harin haɗin gwiwa da Najeriya da Amurka suka kai a watan Mayu, 2027, cewar rahoton The Cable.

A wannan farmaki ne aka kashe Abu Bilal al-Minuki, wanda aka fi sani da Abubakar Mainok, ɗaya daga cikin manyan kwamandojin kungiyar ISWAP.

Sojoji.
Dakarun sojojin Najeirya yayin da suke aikin wanzar da zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya Hoto: Nigerian Army
Source: Twitter

Manyan jami'an gwamnatin Donald Trump sun sha amfani da wannan farmaki a matsayin hujjar nasarar yaƙi da ta’addanci a Najeriya.

Da aka tambayi Janar Uba dalilin da ya sa gwamnatin Najeriya ba ta sanar da jama'a cewa ta miƙa kayayakin ba, ya ce haɗin gwiwar tsaro tsakanin Najeriya da Amurka ba sabon abu ba ne.

Ribadu ya gana da tawagar Amurka

Rahoto ya zo cewa mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya gana da sabon Mataimakin Sakataren Harkokin Wajen Amurka mai kula da Afrika.

Kara karanta wannan

"Ba so muke yi a dakatar da shari'a ba"; Bukatar matar El Rufai ga Tinubu

An gudanar da ganawar ne a Abuja a ranar Litinin 13 ga watan Yuli, 2026 domin ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro tsakanin Najeriya da Amurka.

Ziyarar ta zo ne a lokacin da aka ake samun matsalolin tsaro musamman a Arewacin Najeriya inda yan ta'adda da yan bindiga ke kashe jama'a ba dare ba rana.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262