Yaƙin Amurka da Kasar Musulunci Ta Iran Ya Zama 'Alheri' ga Attajirin Najeriya, Dangote

Yaƙin Amurka da Kasar Musulunci Ta Iran Ya Zama 'Alheri' ga Attajirin Najeriya, Dangote

  • Wani rahoto da aka fitar yau Juma'a, 10 ga watan Yulin 2027 ya nuna alherin da matatar Dangote ta samu sakamakon yakin Amurka da Iran
  • Rahoton ya ce matatar hamshaƙin ɗan kasuwar ta amfana sosai saboda man da take tacewa ba ya bi ta mashigin Hormuz
  • Matatar Dangote na ci gaba da fitar da kayayyakin ta kamar fetur, dizal da man jirgin sama zuwa kasashen duniya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Lagos, Nigeria - Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, na daga cikin manyan wadanda suka amfana da rikicin da ya barke tsakanin Amurka da Iran.

Wani rahoton bincike da aka fitar ya nuna cewa matatar Dangote ta samu alheri a yakin da ya gudana tsakanin Amurka/Isra'ila da Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Matatar Dangote.
Wani bangaren matatar Dangote da ke jihar Legas a Najeriya Hoto: Dangote Refinery
Source: Getty Images

Rahoton, wanda jaridar Wall Street Journal (WSJ) ta wallafa yau Juma'a, ya nuna cewa, Dangote na ci gaba da girbar amfanin matatar man fetur ta Dala biliyan 20 da ya gina.

Kara karanta wannan

Sakon gwamnan Kano, Abba Gida Gida ga lauyoyi game da zaben 2027

Matatar Dangote ta ci gajiyar rikicin Iran

A cewar WSJ, matatar ta kai cikakken karfin aiki tun watan Fabrairun wannan shekara, lamarin da ya ba ta damar samar da fetur, dizal da man jiragen sama ba tare da dogaro da mashigin Hormuz ba.

Rahoton ya ce karuwar bukatar wadannan kayayyakin ta kara wa Dangote dukiyarsa da kusan Dala biliyan 4.86 tun farkon shekarar nan, inda darajar dukiyarsa ta kai kusan Dala biliyan 34.8.

Hakan ya sanya shi cikin jerin mutane mafiya arziki na 65 a duniya, kamar yadda Bloomberg Billionaires Index ta nuna.

Matatar na shirin shiga kasuwar hannun jari

Mataimakin shugaban masana'antun Dangote, Devakumar Edwin, ya shaida wa WSJ cewa kamfanin na shirin sanya matatar fetur a Kasuwar Hannayen Jari ta Najeriya (NGX) kafin karshen shekarar nan.

Ya ce ana sa ran darajar matatar za ta kai akalla Dala biliyan 50, sannan kamfanin na duba yiwuwar sake shiga kasuwar hada-hadar hannayen jari ta New York.

Kara karanta wannan

Farashin mai ya haura Dala 80 bayan Trump ya sake rura rikicin Iran

Bukatar kayayyakin matatar ta karu

Edwin ya bayyana cewa bukatar kayayyakin matatar Dangote ta karu sosai a kasashen yankin Afirka da ke kudancin Sahara, yayin da fitar da man jiragen sama zuwa Turai ma ta karu.

Ya kuma ce kamfanin na shirin fadada matatar zuwa iya tace ganga miliyan 1.4 a rana nan da shekarar 2028, aikin da ake sa ran zai lakume kusan Dala biliyan 13.

Dangote.
Shugaban rukunin kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote Hoto: Aliko Dangote
Source: Getty Images

Dangote zai gina sabuwar matata a Kenya

Baya ga haka, Edwin ya bayyana cewa Dangote na shirin gina wata sabuwar matatar mai a yankin Lamu da ke gabar tekun Kenya.

Ya ce aikin, wanda ya hada da gina tashar ruwa, zai dauki kusan shekara uku ana yi, tare da kashe kusan Dala biliyan 15.

A cewarsa, kamfanin ya riga ya zabi wurin da za a gina matatar kuma yana shirin fara aikin zane da tsarinta.

Matatar Dangote ta fara jigilar fetur kyauta

A wanai rahoton, kun ji cewa matatar Dangote ta fara jigilar fetur kyauta zuwa jihohi shida da Abuja ga masu sayen lita 250,000 ko fiye ba tare da karin kudin sufuri ba.

Kara karanta wannan

Kenya: Dangote ya zabi kasar da zai kafa sabuwar matatar mai a Afrika

Wannan na zuwa ne yayin da matatar Dangote ta ci gaba da sayar da fetur a farashin Naira 1,075 kan kowace lita ga abokan huldarta.

Baya ga kai fetur kyauta, matatar ta ce masu sayen da suka cancanta.za su samu damar biyan kudin mai cikin kwanaki 10 bayan an kai musu kaya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262