Hezbollah Ta Samu Gagarumar Nasara kan Sojojin Israila a Lebanon

Hezbollah Ta Samu Gagarumar Nasara kan Sojojin Israila a Lebanon

  • Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta ana ci gaba da musayar wuta jefi-jefi tsakanin Hezbollah da sojojin Israila a Kudancin Lebanon
  • Kungiyar Hezbollah ta kai hare-hare kan sojojin Israila a Kudancin Lebanon, inda ta yi masu barna mai girma
  • Hezbollah ta kai hare-haren ne ta hanyar amfani da jirage marasa matuka wadanda ke dauke da bama-bamai kan sojojin na Israila

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Kudancin Lebanon - Kungiyar Hezbollah ta kai hare-hare ta hanyar amfani da jirage marasa matuka mau dauke bama-bamai kan sojojin Israila.

Mayakan na Hezbollah sun kashe sojan Isra’ila guda ɗaya, yayin da wani kuma ya ji rauni matsakaici a harin wanda aka kai a Kudancin Lebanon.

Hezbollah ta kashe sojan Israila
Sojojin Israila dauke da bindigogi Hoto: Anadolu
Source: Getty Images

Jaridar The Times of Israel ta kawo rahoton cewa Hezbollah ta kai hare-haren ne a ranar Alhamis, 30 ga watan Afirilun 2026 da safe.

Kara karanta wannan

Amurka ta tafka asara a yaki da kasar Musulunci ta Iran, ta kashe kimanin Dala biliyan 25

Hezbollah ta kashe sojan Israila

Wani jirgi mara matuki daban da ƙungiyar Hezbollah ta harba ya sauka a wani sansanin manyan bindigogi a kan iyaka, inda ya raunata wasu sojoji 12.

Sojan da aka kashe an bayyana sunansa da Sgt. Liem Ben Hamo, ɗan shekara 19, na bataliya ta 13 a rukunin Golani, wanda ya fito daga Herzliya, tashar Aljazeera ta kawo rahoton.

Yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka ta shiga tsakani ta bayyana kamar tana rugujewa yayin da ƙungiyar ta kai wasu hare-haren jirage marasa matuka da rokoki da dama ranar Alhamis.

Isra'ila kuma, a nata ɓangaren, ta kai hare-hare kan ƙungiyar a Kudancin Lebanon, tana mai cewa tana mayar da martani ne ga barazana.

Ma’aikatar lafiya ta Lebanon ta ce hare-haren Isra’ila a Kudancin Lebanon sun kashe mutane tara, ciki har da yara biyu.

Hezbollah ta harba jirage marasa matuka

Yayin lamarin na safiyar yau, Hezbollah ta harba jirage marasa matuƙi guda biyu maƙare da bama-bamai zuwa ga sojojin da ke jibge a ƙauyen Qantara.

Kara karanta wannan

Bayan kisan ministan tsaro, shugaban Mali ya magantu kan zargin juyin mulki

A cewar dakarun Isra’ila (IDF), sojojin sun kakkabo ɗaya daga cikin jiragen, yayin da na biyun ya faɗa kusa da dakarun.

Saukar jirgin mara matuki ya kashe Ben Hamo tare da raunata soja na biyun wanda ya samu rauni matsakaici.

Yayin da ake kwashe waɗanda suka ji rauni, sojojin sun ce sun kai hari kan wasu muhimman wuraren Hezbollah a yankin.

Hezbollah ta kashe sojan Israila
Sojan Israila da aka kashe Hoto: @Israel_katz
Source: Twitter

Hezbollah ta kakkabo jirgin Israila

Hezbollah ta ɗauki alhakin harin, inda ta yi iƙirarin a cikin wata sanarwa cewa ta kai hari kan wasu tankokin yaƙi na Isra'ila guda biyu a Qantara da jirage marasa matuƙa.

Haka kuma ƙungiyar ta ce ta kakkabo wani jirgi mara matuƙi na Isra'ila nau'in Hermes 450 a sararin samaniyar kudancin Lebanon, kuma dakarun IDF sun tabbatar da cewa ɗaya daga cikin jiragensu marasa matuƙi ya kakkabo ta hanyar makami mai linzami na Hezbollah.

Daga baya IDF ta ce ta kaddamar da jerin hare-hare ta sama kan wuraren ayyukan Hezbollah a faɗin Kudancin Lebanon.

'Yan adawan Israila sun hade

A wani labarin kuma, kun ji cewa manyan 'yan adawan Israila guda biyu sun hada karfi da karfi wuri guda don kifar da gwamnatin da Benjamin Netanyahu yake jagoranta.

Kara karanta wannan

An tafka asara: Yadda Iran ta lalata manyan kadarorin Amurka a Gabas Ta Tsakiya

Manyan 'yan adawa a Isra'ila, Naftali Bennett da Yair Lapid sun fitar da sanarwa suna bayyana hadewar jam’iyyunsu.

Naftali Bennett wanda yake tsohon Firaministan Israila ne ya ce za a kira sabuwar jam’iyyar da suka hada da suna Together, kuma shi ne zai jagorance ta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng