Siyasar Najeriya
Kungiyar PDP Action 2023, ta gargadi jam'iyyar PDP da ta guji maimaita kuskuren asarar tikitin takarar Shugaban kasa kan tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku.
Gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu, a ranar Laraba, 1 ga watan Satumba ya nisanta kansa daga ayyukan kamfen da ke alakanta shi da zaben shugaban kasa na 2023.
Gwamnan jihar Bayelsa ya bayyana cewa, Najeriya na fuskantar matsalolin tsaro na siyasa baya ga ta 'yan bindiga, tayar da kayar baya da sauran munanan laifuka.
Jam’iyyar PDP ta yi kira ga Hukumar Yaki da Yiwa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) da ta binciki George Akume kan zamba yayin da yake gwamnan jihar Benue.
'Yan siyasar da ake ganin za su yi takarar tikitin shugaban kasa na jam'iyyar PDP a gabannin zaben 2023 sune Bukola Saraki, Atiku Abubakar, da Aminu Tambul.
Jagoran jam'iyyar PDP a jihar Jigawa a ranar Talata, 31 ga watan Agusta, ya amince da Sule Lamido a matsayin wanda yafi cancanta a zaben shugaban kasa a 2023.
Gwamnatin Filato a ranar Talata, 31 ga watan Agusta, ta karyata ikirarin da ya dunga yawo a shafukan soshiyal midiya cewa gwamna Simon Lalong, ya rufe majalisa.
Nasarawa - Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya rushe gaba ɗaya mambobin kwamitin zartarwa na gwamnatinsa yayin da babban zaben 2023 ke kara kusantowa.
Progressive Consolidation Group ta fara kamfen din ta na mataimakin shugaban kasa Osibanjo don zama dan takarar shugaban kasa na APC a 2023 daga jihar Katsina.
Siyasar Najeriya
Samu kari