Hukumar ICPC Ta Yi Magana, Ta Bayyana Manyan Dalilan Kama Ministan Tinubu da Ya Yi Murabus

Hukumar ICPC Ta Yi Magana, Ta Bayyana Manyan Dalilan Kama Ministan Tinubu da Ya Yi Murabus

  • Hukumar ICPC ta tabbatar da kama tsohon Minista, Geoffrey Uche Nnaji kan zargin gabatar da takardun karatu da na NYSC na bogi
  • Hukumar ta ce an kama shi ne bayan ya ƙi amsa gayyatar bincike da aka aika masa ta hanyoyi daban-daban
  • Babbar Kotun Tarayya ta ba ICPC umarnin kama tsohon ministan, wanda ya yi murbus akwanakin baya, domin ci gaba da bincike

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa (ICPC) ta bayyana cewa akwai manyan dalilai guda biyu da suka sa ta tsare tsohon Ministan Kimiyya, Fasaha da Kirkire-kirkire, Hon. Geoffrey Uchechukwu Nnaji.

Ta ce ta dauki matakin ne bayan tsohon ministan ya gaza amsa gayyatar bincike da aka aika masa a wata takarda mai lamba ICPC/HC/CSTF/GUN/GBT/T.1/VOLV16, ranar 15 ga Mayun 2026.

Kara karanta wannan

Amupitan: Shugaban INEC ya dauko batun satar akwatin zabe da magudi gabanin 2027

Hedkwatar ICPC.
Babban ofishin hukumar yaki da rashawa ta ICPC da ke Abuja Hoto: ICPC
Source: Twitter

Mai magana da yawun ICPC, John Odey, ne ya bayyana hakan jim kadan bayan bullar labarin kama Nnaji yau Laraba, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Dalilan ICPC na kama Uche Nnaji

Ya ce bayan Nnaji ya ki amsa gayyatar hukumar, ICPC ta garzaya Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, inda ta samu umarnin kama shi a karkashin ƙara mai lamba FHC/ABJ/CS/1160/2026.

Hukumar ta ce an kama tsohon ministan ne a ranar Laraba, 1 ga Yulin 2026, a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja bayan isowarsa birnin.

A cewarta, jami'an Hukumar Tsaro ta DSS sun taimaka wajen cafke shi kafin daga bisani aka mika shi ga ICPC domin ci gaba da bincike.

Ana binciken Nnaji kan takardun bogi

ICPC ta bayyana cewa ana binciken Nnaji ne kan zargin gabatar da takardun bogi guda biyu yayin tantance shi a matsayin minista a shekarar 2023.

Kara karanta wannan

ICPC sun cafke tsohon ministan Tinubu mai takarar gwamna a filin jirgin sama

Zarge-zargen sun hada da:

  • Takardar shaidar digiri daga Jami'ar Najeriya da ke Nsukka (UNN) da ake zargin ta bogi ce.
  • Takardar shaidar kammala bautar kasa (NYSC) da ake zargin ba ta inganta ba.

Yadda Nnaji ya ki amsar gayyatar ICPC

Hukumar ICPC ta ce tun farko ta aika wa tsohon ministan gayyata ta hanyar adireshinsa na Abuja da Enugu, sannan ta kuma tura masa ta hanyar adireshin imel dinsa.

Sai dai duk da wadannan matakai, Nnaji bai halarci zaman binciken da aka tsara ba.

Nnaji.
Tsohon ministan kimiyya da fasaha kuma dan takarar gwamnan Enugu na PDP, Uche Nnaji Hoto: @UcheNnaji
Source: Twitter

Hukumar ta tabbatar da cewa an tsare tsohon ministan a hedikwatarta da ke Abuja, inda za a ci gaba da gudanar da bincike, kamar yadda Premium Times.

ICPC ta kuma tabbatar wa jama'a cewa za ta bi wannan shari'a cikin gaskiya da bin doka har zuwa karshe.

Uche Nnaji ya daukaka ƙara

A wani rahoton, kun ji cewa tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji, ya ɗaukaka ƙara kan umarnin kotu da ya ba ICPC damar kama shi bisa zargin jabun takardu.

Kara karanta wannan

Tinubu ya fadi minista 1 da ya fahimci nufin gwamnatinsa ga 'yan Najeriya

Baya ga umarnin kama shi, kotun ta kuma bai wa ICPC damar ayyana Nnaji a matsayin wanda ake nema ta hanyar jaridu, kafafen sada zumunta da sauran shafukan yada labarai.

Nnaji ya daukaka kara a ranar 18 ga Yuni, 2026 kwanaki biyar bayan ya musanta cewa akwai wani umarnin kotu da aka bayar domin kama shi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262