Hukumar ICPC Ta Yi Magana, Ta Bayyana Manyan Dalila! Kama Ministan Tinubu da Ya Yi Murabus

Hukumar ICPC Ta Yi Magana, Ta Bayyana Manyan Dalila! Kama Ministan Tinubu da Ya Yi Murabus

  • Hukumar ICPC ta tabbatarda kama tsohon Minista Geoffrey Uche Nnaji kan zargin gabatar da takardun karatu da na NYSC na bogi
  • Hukumar ta ce an kama shi ne bayan ya ki amsa gayyatar bincike da aka aika masa ta hanyoyi daban-daban
  • Babbar Kotun Tarayya ta ba hukumar ICPC umarnin kama tsohon ministan, wandaya yi murbus kwanakin baya, domin ci gaba da bincike

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa (ICPC) ta bayyana cewa akwai manyan dalilai guda biyu da suka sa aka tsare tsohon Ministan Kimiyya, Fasaha da Kirkire-kirkire, Hon. Geoffrey Uchechukwu Nnaji.

Hukumar ta kuma bayyana cewa ta dauki matakin shari'a ne bayan tsohon ministan ya gaza amsa gayyatar bincike da aka aika masa ta wata takarda mai lamba ICPC/HC/CSTF/GUN/GBT/T.1/VOLV16, ranar 15 ga Mayun 2026.

Kara karanta wannan

Amupitan: Shugaban INEC ya dauko batun satar akwatin zabe da magudi gabanin 2027

Hedkwatar ICPC.
Babban ofishin hukumar yaki da rashawa ta ICPC da ke Abuja Hoto: ICPC
Source: Twitter

Mai magana da yawun ICPC, John Odey,ne ya bayyana hakan jim kadan bayan bullar labarin kama Nnaji yau Laraba, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Ya ce bayan Nnaji ya ki amsa gayyatar hukumar, ICPC ta garzaya Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, inda ta samu umarnin kama shi a karkashin ƙara mai lamba FHC/ABJ/CS/1160/2026.

Hukumar ta ce an kama tsohon ministan ne a ranar Laraba, 1 ga Yulin 2026, a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja bayan isowarsa birnin.

A cewarta, jami'an Hukumar Tsaro ta DSS sun taimaka wajen cafke shi kafin daga bisani aka mika shi ga ICPC domin ci gaba da bincike.

Ana bincikensa kan takardun bogi

ICPC ta bayyana cewa ana binciken Nnaji ne kan zargin gabatar da takardun bogi guda biyu yayin tantance shi a matsayin minista a shekarar 2023.

Zarge-zargen sun hada da:

Kara karanta wannan

ICPC sun cafke tsohon ministan Tinubu mai takarar gwamna a filin jirgin sama

  • Takardar shaidar digiri daga Jami'ar Najeriya da ke Nsukka (UNN) da ake zargin ta bogi ce.
  • Takardar shaidar kammala bautar kasa (NYSC) da ake zargin ba ta inganta ba.

Ya ki amsa gayyatar bincike

Hukumar ta ce tun farko ta aika wa tsohon ministan gayyata ta hanyar adireshinsa na Abuja da Enugu, sannan ta kuma tura masa ta hanyar adireshin imel dinsa.

Sai dai duk da wadannan matakai, Nnaji bai halarci zaman binciken da aka tsara ba.

ICPC ta ce bincike zai ci gaba

Hukumar ta tabbatar da cewa an tsare tsohon ministan a hedikwatarta da ke Abuja, inda za a ci gaba da gudanar da bincike.

ICPC ta kuma tabbatar wa jama'a cewa za ta bi wannan shari'a cikin gaskiya da bin doka har zuwa karshe.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262