Zargin Badakalar N400m: Atiku Ya Bukaci Tinubu Ya Kori Shugaban Ma’aikatansa
- Dan takarar shugaban kasa a ADC, Atiku Abubakar ya nuna damuwa game da karuwar cin hanci da rashawa a Najeriya
- Atiku ya bukaci Shugaba Tinubu ya dakatar da Femi Gbajabiamila tare da binciken zargin karɓar Naira miliyan 400
- Gbajabiamila ya musanta sanin PFIPC ko naɗa Adeniyi Adeyemi, yayin da Adeyemi ke zarginsa da neman kaso daga kuɗin fara aikin hukumar
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Atiku Abubakar, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC, ya yi magana magana game da zargin na kusa da Bola Tinubu da badakala.
Atiku ya bukaci Shugaba Bola Tinubu da ya dakatar da Shugaban Ma'aikatansa, Femi Gbajabiamila, bisa zargin karɓar Naira miliyan 400.

Source: Getty Images
Hakan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Paul Ibe, ya fitar a shafin X a jiya Talata 30 ga watan Yunin 2026.
Shawarar da Atiku ya ba gwamnatin Tinubu
Ana zargin an yi badakalar ta hannun wani wakili tare da neman ƙarin Naira miliyan 200 domin sauƙaƙa naɗin Adeniyi Adeyemi a matsayin babban daraktan Hukumar PFIPC.
Atiku ya ce ya kamata Tinubu ya jagoranci gwamnati ta hanyar tabbatar da cewa duk jami'ansa suna fuskantar hukunci idan aka samu zarge-zargen cin hanci ko rashin gaskiya.
Ya ce ikirarin da Gbajabiamila ya yi na cewa PFIPC ba ta wanzu a matsayin hukuma ya ƙara jefa gwamnatin cikin matsala, domin an ware mata Naira biliyan 27.4 a kasafin kuɗin shekarar 2026.
Atiku ya kalubalanci yadda za a ware irin wannan makudan kuɗi ga wata hukuma da ake cewa ba ta wanzu ba.

Source: Twitter
Kiran da Atiku ya yi ga Tinubu
Atiku ya jaddada cewa shugabanci nagari yana dogara ne kan gaskiya da ɗaukar alhaki, yana mai cewa ba za a iya cimma hakan ba idan ana kare abokai da 'yan uwa masu rike da mukamai.
Tun da farko, Adeniyi Adeyemi ya yi zargin cewa Gbajabiamila ya nemi kashi 48 cikin 100 na kuɗin fara aikin PFIPC da ya kai Naira biliyan 27.4.
Adeyemi ya ce ya ƙi amincewa da wannan buƙata bayan an riga an karɓi Naira miliyan 400 ta hannun wakili, yayin da ake neman ƙarin Naira miliyan 200 domin tabbatar da naɗinsa.
Sai dai a martaninsa da ya fitar a ranar 11 ga Yunin 2026, Gbajabiamila ya musanta duk wata alaƙa da PFIPC, yana mai cewa babu irin wannan hukuma a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu, kuma bai san wani naɗin Adeyemi ba.
Atiku ya zargi ana shirya masu gadar zare
An ji cewa dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar ADC Alhaji Atiku Abubakar ya yi zargin cewa ana ana kulla wani shiri da zai hana jam'iyyarsa shiga zaben 2027.
Atiku Abubakar ya bayyana cewa sun bankado akwai yunkurin amfani da shari'a da hukumomi wajen raunana jam'iyyar adawa.
Ya bayar da shawara ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da bangaren shari'a a kan yadda za su kauce wa zama 'yan abi yarima.
Asali: Legit.ng

