Siyasar Najeriya
Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya sauka kan tsohon ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, inda ya masa tatas kan zargin da ya masa, yace Amaechi ya gaza ta ko ina.
Kungiyar Peter Obi Support Group za ta maida hankali a kan wasu jihohi ne a zaben shugabancin kasa. Kusan dukkanin jihohin su na yankin Arewacin Najeriya ne.
Jaridar Thisday ta ruwaito cewa mambobin na jam’iyyar APC wadanda aka ce ba su gaza 5,000 ba sun saki jam'iyyar su Buhari kuma mai mulki a jihar zuwa ta adawa.
Sanata Emmanuel Orker-Jev, ya ce jam’iyyar PDP na iya tsintar kanta a cikin manyan rikice-rikice’ idan har shugabanta na kasa, Iyorchia Ayu, ya yi murabus.
Jam’iyyar adawa ta PDP ta bayyana cewa, reshenta a jihar Katsina ya karbe ofisoshin yakin neman zaben shugaban kasa Muhammadu Buhari a jihar ta Katsina a Arewa.
Rundunar 'yan sandan jihar Kano ta damke shugaban jam'iyyar PDP na Fagge da sakataren jam'iyyar tare da kai su kotu kan zargi hada baki da karya kan Abacha.
Shugaban matasan jam'iyyar APC reshen jihar Anambra, Hon Innocent Nwanwa, ya rasa muƙaminsa biyo bayan sauya sheƙar asalin uwar gidansa, Sanata Stella, zuwa PDP
Tawagar yaƙin neman zaɓen ɗan takarar kujera lamba ɗaya a Najeirya karkashin inuwar NNPP, Kwankwaso, ta ƙaryata labarin cewa zai janye wa Tinubu, ko Atiku.
A wata wasika ta musamman da ya rubuta da nufun ankarar da yan Najeriya, Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP, yace zaɓi biyu ya rage wa mutane a babba zaɓen 2023.
Siyasar Najeriya
Samu kari