Rikicin PDP
Kwanaki ƙadan bayan wasu daga cikin yan PDP sun koma APC a jihar Kaduna, shugabanta, Edward Masha, ya ce daman sun ci amanar jam'iyyar a zaben 2023.
Kungiyar matasan NYFA ta ce rikicin PDP ba zai hana Atiku takara a 2027 ba, ta bukaci shugabanni su hada kai don ceto jam’iyya daga barazanar wargajewa.
Gwamnan jihar Ribas, Siminalyi Fubara ya bayyana cewa a hangensa Allah ya toshe duk wani yunƙurin sasanta rikicinsa da Wike domin shi da jama'ar jihar su samu ƴanci.
PDP ta fara sayar da fom ɗin takarar gwamnan Anambra, zaɓen fidda gwani zai gudana 5 ga Afrilu, yayin da za a mika sunan ɗan takara zuwa ga INEC a ranar 22 ga Mayu.
Mukaddashin shugaban PDP na kasa, Ambasa Umar Iliya Damagum ya musanta cewa akwai rashin jituwa a tsakaninsa da sabon sakataren jam'iyya na kasa da aka nada.
Ana zargin 'yan bangar siyasa da jam'iyyar PDP ta yi hayarsu, sun kashe shugaban karamar hukumar Irewole, jihar Osun lokacin da fada ya barke kan hukuncin kotu.
'Yan majalisar dokokin Kaduna sun sauya sheka daga PDP zuwa APC saboda nasarorin Gwamna Uba Sani, suna mai alkawarin ci gaba da kawo zaman lafiya da ci gaba a jihar.
Jam’iyyar PDP a Kudu maso Kudu ta shiga rikici kan taro a Benin. Cif Omemu ya kira shugabanni su kauracewa taron, yana zargin an kulla wata makarkashiya.
Jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya ta dakatar da shugaban kwamitin amintattu (BoT), Sanata Adolphus Wabara. Jam'iyyar ta fadi laifukan da ake zarginsa da su.
Rikicin PDP
Samu kari