Arewa
Wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa dakarun tsaro sun ƙara ƙaimi wajen farautar shugaban ƴan bindiga Kachalla Dan Mai Kinni, bayan cafke yaronsa, Lawali Malangaro.
Rahotanni sun tabbatar da cewa Sojojin 'Operation Fansan Yanma' sun kashe 'yan ta'adda 12 a kauyen Maigora, Faskari, suka kwato babura da dama daga hannunsu.
Rundunar ‘yan sanda ta Jigawa ta kama Rukayyah Amadu bisa laifin kashe kishiyarta, tare da fara bincike kan kisar amarya a Hadejia da almajiri a garin Gwaram.
Sabon rahoto ya nuna cewa tsohon shugaban kasar Nijar, Ibrahim Baré Maïnassara ne ya kafa rundunar Lakurawa a 1997 domin yaki da masu satar shanu.
Gwamnan jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed ya sanar da rasuwar kawunsa kuma Sarkin Alkaleri, Alhaji Muhammadu Abdulkadir, wanda ya rasu yana da shekaru 100.
Rundunar tsaro ta dakile harin ramuwar gayya na ‘yan bindiga a Mada, karamar hukumar Gusau, jihar Zamfara inda ta yi nasarar hallaka hatsabibin dan ta'adda.
Alhaji Attahiru Bafarawa ya musanta shiga SDP, yana mai cewa labaran ba su da tushe. Ya shaida cewa yanzu ya mayar da hankali kan gina rayuwarsa a wajen siyasa.
Gwamnan jihar Jigawa ya kai ziyarar gani da ido kan yadda shirin raba abinci na watan azumin Ramadan ke guduwa. Gwamnan ya nuna damuwa kan abin da ya gani.
Kotun Adamawa ta dage shari’ar da ke kalubalantar kafa Masarautar Fufore. Lauyan masu kara ya nemi karin lokaci don martani ga takardar da gwamnatin jiha ta gabatar.
Arewa
Samu kari