Daga Karshe Trump Ya Fadi Kasar da Za a Dorawa Alhakin Kashe Mutane a Gabas Ta Tsakiya
- Donald Trump ya ce Iran ya kamata ta biya diyya kan asarar rayuka da barna da aka yi wa mutane a Lebanon, Syria, Yemen da Gaza
- Trump ya ce Amurka za ta nemi Iran ta biya diyya kan rikice-rikicen da ya ce Tehran ta shiga a yankin Gabas ta Tsakiya
- Ya ce ya umarci wakilansa su sanya batun biyan diyya cikin duk wata tattaunawa da za a yi nan gaba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Birnin Washington, Amurka - Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ya kamata a rike Iran da alhakin “barnar da aka yi da mutanen da suka mutu” a Lebanon, Syria, Yemen da Gaza.
Trump ya kara da wannan magana ne bayan kalaman da ya yi a baya cewa Amurka za ta nemi Iran ta biya diyya kan rikice-rikicen da ya ce Tehran ta shiga.

Source: Getty Images
Trump ya bayyana hakan ne a wani rubutu da ya yi a shafinsa na Truth Social a ranar Litinin, 10 ga watan Agustan 2026.
Kalaman Trump na zuwa ne bayan Iran ta nemi a biya ta diyya kan barnar da Amurka da Isra’ila suka haddasa yayin yakin da aka kwashe watanni ana yi.
Trump ya nemi diyya daga Iran
Donald Trump ya ce Amurka za ta nemi Iran ta biya diyya bayan Tehran ta nemi a mayar mata da kudin barnar da Amurka da Isra’ila suka yi mata yayin yakin.
A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce Iran na neman diyya, amma ya ce Tehran “ba ta taba ambaton biya ta diyya ba” a tattaunawar da aka yi a baya ko kuma ganawar da aka gudanar.
Trump ya ce shi ma yana neman Iran ta biya diyya kan mutanen da ya ce Iran ta kashe ko ta jikkata sosai da bama-baman da ake dasasu a gefen hanya da kuma wasu rikice-rikice.

Kara karanta wannan
Trump ya fusata, ya yi ƙarin haske kan jita jitar cewa suna fama da ƙarancin makamai
Ya kuma hada da iyalan mutanen da aka kashe a harin da aka kai kan jirgin ruwan sojin Amurka USS Cole, da kuma dubban wasu da aka kashe a fagen daga.
An bukaci diyya ga masu zanga-zanga
Trump ya ce Iran ya kamata ta kuma biya diyya ga iyalan masu zanga-zangar da aka kashe a kasar cikin shekaru 50 da suka gabata.
Ya kuma ce ya kamata a biya iyalan daruruwan dubban masu zanga-zangar da ba su ji ba, ba su gani ba” da ya ce Iran ta kashe a cikin shekaru 50 da suka gabata, baya ga mutane 52,000 da ya ce an kashe cikin watanni biyar da suka gabata.
Trump ya umarci wakilansa
Trump ya ce ya umarci wakilansa su tabbatar da cewa batun biyan diyya ya kasance wani bangare na duk wata tattaunawa da za a yi nan gaba.
“Na umarci wakilaina su sanya wannan batu cikin duk wata tattaunawa da za a yi nan gaba.” In ji shi.

Source: Facebook
Iran ta nada sababbin kwamandoji
A wani labarin kuma, kun ji cewa jagoran Iran kuma kwamandan askarawan kasar, Mojtaba Hosseini Khamenei, ya sanar da nada manyan kwamandojin soji shida.
Kwamandojin za su aiki ne a wasu muhimman mukamai a rundunar sojin kasar, Rundunar Kare Juyin Juya Halin Musulunci (IRGC) da kuma rundunar Basij.
Asali: Legit.ng
