Mataimakin Gwamnan Kano Ya Haifar da Ruɗani a Rikicin Sarauta tsakanin Aminu Ado da Sanusi II
- Mataimakin gwamnan Kano, Murtala Sule Garo, ya halarci Mauludin Sheikh Ahmad Tijjani, wanda aka gudanar a fadar Aminu Ado Bayero
- An gudanar da taron ne a daidai lokacin da takaddamar masarautar Kano ke ci gaba tsakanin Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II
- Masu halartar Mauludin sun nuna damuwa kan rashin amincewa da amfani da filin wasa na Sani Abacha
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria - Mataimakin gwamnan jihar Kano, Murtala Sule Garo, ya halarci Mauludin Sheikh Ahmad Tijjani na shekara-shekara da aka gudanar a fadar Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ranar Lahadi.
Taron ya samu halartar malamai, mabiya darikar Tijjaniyya da sauran masu ibada daga Kano da jihohin makwabta, har ma da yan kasashen waje.

Source: Facebook
Jaridar Punch ta rahoto cewa an gudanar da taron ne a daidai lokacin da takaddamar sarautar Kano tsakanin Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II ke ci gaba.
Murtala Garo ya halarci taron Sarki Aminu
Halartar Garo ta dauki hankali saboda Aminu Bayero da Sanusi na ci gaba da kasancewa a tsakiyar rikicin masarautar Kano.
Aminu Ado Bayero na samun goyon bayan wani bangare da ke da alaka da tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje, yayin da gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ke goyon bayan Muhammadu Sanusi II.
An gudanar da Mauludin a fadar Nasarawa inda Aminu Ado ke zaune duk da cewa gwamnatin jihar ta amince da Sanusi II a matsayin sarki bayan dawo da shi kan karagar mulki a watan Mayun 2024.
An gudanar da Mauludi a fadar Bayero
A baya, an yi yunkurin gudanar da Mauludin a filin wasa na Sani Abacha, amma rahotanni sun nuna cewa ba a samu amincewar gwamnatin jihar cikin lokaci ba.
A nasa bangaren, kakakin Sarki Aminu Ado Bayero, Abubakar Balarabe Kofar Na’isa, ya ce mataimakin gwamnan ya wakilci Gwamna Abba Kabir Yusuf a wajen taron.
Sai dai ya bayyana cewa mutanen da suka raka mataimakin gwamnan ba jami’an gwamnati ba ne, illa dai wasu daga cikin magoya bayansa.
Kofar Na’isa ya ce masu shirya Mauludin sun rubuta wa ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Kano da kuma na mai ba gwamnan shawara kan harkokin addini domin neman izinin amfani da filin wasan Sani Abacha, amma hakan ba ta samu ba.

Source: Facebook
Mauludin ya tara dumbin mutane
Wani mazaunin Kano, Ilyasu Idris, ya ce taron ya nuna cewa darikar Tijjaniyya na ci gaba da samun dimbin mabiya a jihar.
Ya ce abin da ya fi muhimmanci shi ne an gudanar da Mauludin cikin kwanciyar hankali, inda mutane suka samu damar haduwa domin addu’o’i da sauran ayyukan ibada.
Jawabin Tinubu a Maulidin Sheikh Tijjani
A wani labarin, kun ji cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tura wakili wurin maulidin Sheikh Ahmad Al-Tijani, RTA, wanda ya gudana a jihar Kano.
A jawabin da ya tura, Tinubu ya bukaci shugabannin Tijjaniyya da mabiyansu na duniya su fito su rika sukar ayyukan ta'addanci da tsattsauran ra'ayi.
Ya kuma bukaci kungiyoyin addini da hanyoyin sadarwarsu su kara karfafa wayar da kan jama’a kan zaman lafiya, ilimin addini, karatu da kuma tarbiyyar matasa masu nagarta.
Asali: Legit.ng

