Yan ta'adda
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar sheke 'yan ta'adda a wani samame da suka kai dajin Sambisa cikin jihar Borno. Sojojin sun kuma kwato makamai.
Wasu miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun kai sabon hari a jihar Sokoto. Miyagun 'yan bindigan sun sace almajirai masu tarin yawa a yayin farmakin da suka kai.
Jami'an rundunar sojin Najeriya sun yi nasarar murƙushe ɗaruruwan yan ta'adda a sassa daban-daban na ƙasar nan, sun kamo wasu sama da 100, sun ceto mutum 46.
Jama'a sun shiga tashin hankali bayan mahara sun yi ajalin jami'an 'yan sanda hudu a jihar Ebonyi tare da hallaka 'yan matansu biyu yayin harin a birnin Abakaliki.
Hedkwatar tsaron Najeriya ta bayyana cewa dakarun sojoji sun shirya tunkarar kowace irin barazana idan bukatar hakan ta taso musamman a watan Ramadan.
'Yan majalisar wakilai sun yi Allah wadai da nuna takaici kan sace mata sama da 300 da aka yi a jihar Borno. Sun bukaci jami'an tsaro su gaggauta ceto su.
Duba da yadda ake fama da matsalar tsaro a Abuja, Minista Nyesom Wike ya yi magana kan makiyaya da ke kiwo a tsakiyar birnin inda ya ce zai dauki mataki.
Ministan tsaron Najeriya, Muhammad Badaru, ya bayyana irin yadda rundunar sojojin Najeriya ke ci gaba da samun galaba kan masu tada ƙayar baya a faɗin kasar nan.
Tsagerun 'yan ta'addan Boko Haram sun yi awon gaba da mata 'yan gudun hijira har mutum 319 a wani sabok farmaki da suka kai a jihar Borno ta Najeriya.
Yan ta'adda
Samu kari