Darussan da Marigayi Buhari Ya Koya wa Ƴaƴansa Lokacin da Yake Raye

Darussan da Marigayi Buhari Ya Koya wa Ƴaƴansa Lokacin da Yake Raye

  • Yar marigayi Muhammadu Buhari ta bayyana kyawawan halayen tsohon shugaban kasar Najeriya
  • Hanan Buhari ta ce marigayi mahaifinta, Buhari, ya koya mata muhimmancin gaskiya, juriya da hidimar al'umma,
  • Ta bayyana haka ne bayan karɓar lambar yabo a taron shugabanci da kasuwanci da aka gudanar a Morocco

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Marrakech, Morocco - Hanan Buhari, 'yar marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ta tuna kyawawan halayen mahaifinta.

Hanan ta ce mahaifinta ya koya mata darussan gaskiya, juriya da hidimar jama'a ba tare da son kai ba.

Yar Buhari ta faɗi darasin da ta koya daga mahaifinta
Yar marigayi Muhammadu Buhari da wasu baki yayin taro a Morocco. Hoto: Hanan Buhari.
Source: Twitter

Hanan ta yi wannan bayani ne a birnin Marrakech na ƙasar Morocco bayan karɓar lambar yabo ta 100 Most Notable Peace Icons of Africa, cewar The Nation.

A wata sanarwa da Daraktan aikin taron, Kingsley Amafibe, ya fitar, Hanan ta sadaukar da wannan lambar yabo ga marigayi mahaifinta cikin alhini.

Kara karanta wannan

DSS da yan sanda sun yi bincike, an ji gaskiya kan ɓullar sabuwar ƙungiyar ta'addanci a Najeriya

Ta bayyana cewa irin tarbiyyar, horo da amincewar da mahaifinta ya nuna mata ne suka taimaka wajen gina rayuwarta da kuma ƙarfafa mata gwiwar cimma buri.

Ta ce:

"Na sadaukar da wannan karramawa ga marigayi mahaifina, Shugaba Muhammadu Buhari, wanda shawararsa, horonsa da amincewarsa da ni suka gina macen da na zama.
"Ya koya min muhimmancin gaskiya, juriya da hidimar al'umma ba tare da son kai ba. Amincewarsa da ni ta ba ni ƙarfin gwiwar yarda da kaina."

Hanan ta ce za ta ci gaba da kare ƙa'idojin da mahaifinta ya koyar da ita ta hanyar ƙarfafa mata da kuma bayar da gudunmawa mai amfani ga al'umma.

Amafibe ya taya Hanan Buhari murnar wannan karramawa, yana mai bayyana ta a matsayin abin koyi da ke ƙarfafa sabon ƙarni na shugabannin Afirka.

Ya ce jajircewarta wajen bunƙasa rayuwar mata na ci gaba da zaburar da matasa da dama a nahiyar wajen neman shugabanci nagari da ci gaba.

An shirya taron ne ƙarƙashin gidauniyar DAVDAN Peace and Advocacy Foundation da 100 Most Notable Peace Icons Africa tare da halartar shugabanni da 'yan kasuwa.

Kara karanta wannan

Ambaliya ta mamaye yankunan Legas, hanyoyi sun yi makil, lantarki ta katse

Haka kuma masu tsara manufofi, jami'an diflomasiyya da sauran manyan baƙi daga sassa daban-daban na Afirka sun halarci taron domin karrama fitattun mutane.

Taron ya mayar da hankali ne kan yabawa waɗanda suka bayar da gagarumar gudunmawa wajen shugabanci, samar da zaman lafiya, kasuwanci da bunƙasa ci gaba mai ɗorewa a nahiyar.

Haka kuma masu tsara manufofi, jami'an diflomasiyya da sauran manyan baƙi daga sassa daban-daban na Afirka sun halarci taron domin karrama fitattun mutane.

Taron ya mayar da hankali ne kan yabawa waɗanda suka bayar da gagarumar gudunmawa wajen shugabanci, samar da zaman lafiya, kasuwanci da bunƙasa ci gaba mai ɗorewa a nahiyar.

Yadda Hanan ta bude Gidauniya a Kaduna

A baya, an ji cewa Hanan Buhari, daya daga cikin 'yayan shugaba Muhammadu Buhari ta yi Alla-wadai da yadda ake fyade a Najeriya.

Hanan ta kaddamar da sabuwar gidauniyar kare hakkin yara da mata da ake cin zarafi a Najeriya wanda ya ke daya daga cikin matsalolin da ake fama da su.

Yar marigayi Muhammadu Buhari tana auren Muhammad Turad Sha'aban, 'dan tsohon dan takaran kujerar gwamnan jihar Kaduna.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.