NDC: Hanyar da Jam'iyyar Su Kwankwaso Za Ta Tattara Kudin Yakin Neman Zabe

NDC: Hanyar da Jam'iyyar Su Kwankwaso Za Ta Tattara Kudin Yakin Neman Zabe

  • NDC ta ce za ta bai wa ’yan Najeriya damar bayar da gudummawar kuɗi daga N1,000 domin tallafa wa ayyukan jam’iyyar da shirye-shiryenta na zaɓen 2027
  • Seriake Dickson ya ce bai kamata a bar attajirai da masu amfani da dukiyar gwamnati su mallaki tsarin dimokuraɗiyyar Najeriya ba
  • Jam’iyyar ta ce tana tattaunawa kan mambobin kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa, yayin da ta buƙaci INEC ta tabbatar da zaɓe mai inganci a 2027

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) ta bayyana hanyar da za ta tattara kudaden yakin neman zaben 2027.

Jam'iyyar NDC ta ce za ta nemi gudummawar kuɗi daga talakawan Najeriya domin rage tasirin masu hannu da shuni a tsarin dimokuraɗiyyar ƙasar.

Sanata Dickson ya yi magana kan NDC
Jagoran NDC na kasa, Sanata Seriake Dickson Hoto: @IamHSDickson
Source: Facebook

Jagoran jam’iyyar na ƙasa, Seriake Dickson, ne ya bayyana hakan ranar Laraba, 9 ga watan Satumban 2026 yayin wata hira da shirin Prime Time na tashar Arise News.

Kara karanta wannan

Zaben 2027: Kungiyar APC ta yi barazanar fallasa sanata Ali Modu Sheriff

Za a karɓi gudummawar N1,000

Dickson, wanda ke wakiltar Bayelsa ta Yamma a Majalisar Dattawa, ya ce NDC za ta bai wa ’yan Najeriya damar bayar da gudummawar kuɗi kaɗan, kamar N1,000 ko N2,000, domin tallafa wa ayyukan jam’iyyar.

Ya bayyana NDC a matsayin jam’iyyar siyasa ɗaya tilo a Najeriya da ba ta samun kuɗaɗen gudanarwarta daga baitulmalin gwamnati.

“Ba za ku bar dimokuraɗiyyarku ta dogara da attajirai da hamshaƙan ’yan kasuwa ba, waɗanda yanzu suka zama masu tiriliyan ta hanyar amfani da albarkatun gwamnati. Za a ci gaba da nuna maku danniya,” in ji Dickson.

Ya ce manufar jam’iyyar ita ce ƙarfafa talakawa da mutanen da ake zalunta domin su samu damar taka rawa a harkokin siyasa.

“Muna son samar da tsarin da ’yan Najeriya, talakawa ’yan Najeriya, za su iya bayar da N1,000 ko N2,000, kamar yadda ake yi a sauran ƙasashen duniya,” in ji shi.

Kara karanta wannan

Shugaban APC na kasa ya tafi hutu, zai yi gagarumin shiri don zaben 2027

NDC na shirin kafa kwamitin yaƙin neman zaɓe

Dickson ya kuma bayyana cewa jam’iyyar na ci gaba da tuntubar juna kan waɗanda za su kasance cikin kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na NDC.

Ya ce za a sanar da sunayen mambobin kwamitin nan ba da jimawa ba, yana mai cewa jam’iyyar ba ta son maimaita abin da wata jam’iyyar da ke mulki ta yi.

“Ba ma son yin abin da sauran jam’iyyar da ke gwamnati ta yi, wato ta wallafa wani abu sannan ta janye shi,” in ji shi.

Ya buƙaci INEC ta tabbatar da zaɓe mai inganci

Shugaban NDC ya buƙaci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), hukumomin tsaro da sauran hukumomin da abin ya shafa su tabbatar da gudanar da zaɓe cikin ’yanci, gaskiya da adalci a 2027.

Dickson ya ce NDC za ta gabatar da manufofinta ga ’yan Najeriya, tare da yin gwagwarmaya kan kowace ƙuri’a a lokacin zaɓen.

“Za mu gabatar da batunmu ga al’ummar Najeriya, kuma za mu yi yaƙi kan kowace ƙuri’a. Za a fafata kan kowace ƙuri’a,” in ji shi.

Kara karanta wannan

Dan takara ya yi alkawarin samar da lantarki a kowane gida cikin watanni 11 a Najeriya

Dickson ya yi magana kan NDC
Sanata Seriake Dickson na mika tutar NDC ga Peter Obi Hoto: @IamHSDickson
Source: Facebook

Kwankwaso ya aika sako ga Atiku

A wani labarin kuma, kun ji cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya aika da saƙo ga tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar game da siyasa.

Sanata Kwankwaso ya ce Atiku, wanda ke riƙe da sarautar gargajiya ta Waziri Adamawa, ya kamata ya koma ya kula da wannan matsayi na gargajiya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng