2027: Jam'iyyar NDC Ta Su Kwankwaso Ta Fitar da Sunayen Yan Takarar Gwamna a Jihohi 12
- Jam'iyyar NDC ta musanta rahoton cewa ba ta da yan takarar gwamna a jihohi 12 yayin da zaben 2027 ke kara kusantowa
- Mai magana da yawun NDC na kasa ya tabbatar da cewa jam'iyyar ta tsaida yan takarar gwamna a jihohi 28 da za a fafata a zaben 2027
- NDC ta ce ita kungiyar siyasa ce ta kasa baki daya mai tsari, 'yan takara da magoya baya a dukkan jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya, Abuja
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Jam'iyyar adawa ta NDC ta karyata rahotannin da ke cewa ba ta da 'yan takarar gwamna a jihohi 12 gabanin babban zaben 2027.
Jam'iyyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da sakataren yada labaranta na kasa, Osa Director, ya fitar ranar Asabar, 5 ga watan Satumban 2026.

Source: Facebook
Mai magana da yawun NDC ya bayyana rahotannin a matsayin karya da kuma masu yaudarar jama'a, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.
NDC ta tsaida yan takara a jihohi 28
NDC ta jaddada cewa ta tsayar da 'yan takarar gwamna yadda ya kamata a dukkan jihohi 28 da za a gudanar da zaben gwamna a cikinsu a shekarar 2027.
Mist Osa Director ya ce:
“Domin kawar da duk wata shakka, NDC ta tsayar da 'yan takarar gwamna yadda ya kamata a dukkan jihohi 28 da za a gudanar da zaben gwamna a cikinsu a shekarar 2027.”
Jam'iyyar ta ce ita kungiyar siyasa ce ta kasa baki daya mai tsari, 'yan takara da magoya baya a dukkan jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya, Abuja.
Ta ce:
“NDC ba jam'iyyar wani yanki ba ce. Mu yunkuri ne na kasa baki daya mai 'yan takara, tsari da magoya baya a dukkan jihohi 36 da FCT.”

Kara karanta wannan
Kwankwaso ya ware gwamnonin Arewa, ya fadi matsalan da za su fuskanta a zaben 2027
Sunayen takarar NDC a jihohi 12
Jam'iyyar ta bayyana sunayen 'yan takararta na gwamna a jihohi 12 da aka ce rahotannin sun yi ikirarin ba ta da 'yan takara kamar haka:
- Jihar Zamfara – Sanata Kabiru Marafa
- Jihar Borno – Rear Admiral Ibrahim Sanusi Kasim mai ritaya
- Jihar Cross River – Hon. John Odey
- Jihar Akwa Ibom – Babanta Michael Okon
- Jihar Ebonyi – Nwofe Boniface
- Jihar Filato – Yakubu Solomon Ndam
- Jihar Katsina – Ilu-Barde Aliyu
- Jihar Kebbi – Alhaji Umar Usman Besse
- Jihar Yobe – Jonga Yahaya Gabakau
- Jihar Jigawa – Dutse Aminu Sani
- Jihar Taraba – Farfesa Yahaya Mohammed Sani
- Jihar Neja – Abdu Sidi Bomi
NDC ta ja hankalin yan jarida
NDC ta kuma bukaci kafafen yada labarai, 'yan jarida, masu rubutun shafukan intanet da masu kirkirar abubuwan da ake yadawa a kafafen sada zumunta su tabbatar da sahihancin bayanai kafin wallafa su.

Source: Twitter
A riwayar Vanguard, jam'iyyar ta ce:
“Muna kira ga gidajen yada labarai, 'yan jarida, masu rubutun shafukan intanet da masu kirkirar abubuwan da ake yadawa su binciki majiyoyinsu tare da tabbatar da sahihancin bayanai kafin wallafa su.
Ta yi gargadin cewa yada bayanan da ba a tabbatar da sahihancinsu ba na iya raunana amincewar jama'a da kafafen yada labarai da kuma tsarin dimokuradiyya.
Peter Obi ya shirya kare kuri'un NDC
Kun ji cewa dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Nigeria NDC, Peter Obi, ya bayyana cewa a shirye yake ya rasa ransa domin kare kuri'unsa a zaben 2027.
Obi ya sha alwashin cewa duk waɗanda ke.shirin murɗe zaɓe mai zuwa ba za su samu nasara ba, inda ya ƙara da cewa babu wanda zai sake tsoratar da mutane.
Asali: Legit.ng

