Nentawe: Shugaban APC na Kasa Ya Tafi Hutu, Zai Yi Gagarumin Shiri don Zaben 2027

Nentawe: Shugaban APC na Kasa Ya Tafi Hutu, Zai Yi Gagarumin Shiri don Zaben 2027

  • Shugaban APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya fara hutun makonni biyu a ƙasashen waje domin samun hutu da sake tsara dabarunsa
  • Jam’iyyar ta ce Yilwatda ya shafe shekararsa ta farko yana gudanar da tafiye-tafiye, shawarwari da tarurrukan dabarun ƙarfafa APC gabanin 2027
  • APC ta ce rashin shugaban a ƙasar ba zai kawo cikas ga tafiyar da jam’iyyar ba, domin NWC zai ci gaba da gudanar da ayyuka bisa kundin tsarin jam’iyyar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya fara hutun makonni biyu a ƙasashen waje bayan shafe shekara guda yana gudanar da ayyukan jam’iyya masu yawa.

A cewar jam’iyyar, hutun zai ba Yilwatda damar samun hutu, sake kuzari da kuma yin tunani kan manyan ayyukan da ke gabansa yayin da ake shirin zaɓen 2027.

Kara karanta wannan

Dan takara ya yi alkawarin samar da lantarki a kowane gida cikin watanni 11 a Najeriya

Farfesa Nentawe zai tafi hutu
Farfesa Nentawe Yilwatda na jawabi a wajen taro Hoto: Senator Uba Sani
Source: Facebook

Abimbola Tooki, mai ba shugaban APC shawara na musamman kan yaɗa labarai da dabarun sadarwa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Laraba, 9 ga watan Satumban 2026 a shafin X.

Yilwatda ya shafe shekara yana ayyukan jam’iyya

Sanarwar ta ce shugaban APC ya shafe shekarar farko ta wa’adinsa yana gudanar da ayyuka da dama da suka haɗa da tafiye-tafiye, shawarwari da ganawa da masu ruwa da tsaki.

Tun bayan da ya karɓi shugabancin jam’iyyar, Yilwatda ya yi aiki tare da Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC), gwamnoni, ’yan Majalisar Dokoki ta Ƙasa, shugabannin APC na jihohi da sauran zaɓaɓɓun jami’ai.

Manufar waɗannan ayyukan, a cewar jam’iyyar, ita ce ƙarfafa APC da kuma sake tsara ta domin tunkarar zaɓen 2027.

APC ta bayyana nasarorin shugabancinsa

Jam’iyyar ta lissafa nasarar shirya da kammala Babban Taron Ƙasa na APC, ƙarfafa tsarin cikin gida na jam’iyyar da kuma gudanar da zaɓukan fidda gwani a matakai daban-daban.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya ware gwamna a Arewa ya kwararo masa yabo

APC ta ce waɗannan nasarorin, waɗanda aka samu cikin ɗan kankanin lokaci, sun ƙara tabbatar da matsayin jam’iyyar a matsayin babbar jam’iyyar siyasa a Najeriya.

Hutun ba ya nufin ya bar aikinsa

Jam’iyyar ta jaddada cewa bai kamata a ɗauki hutun Yilwatda a matsayin ya janye daga aikinsa ba.

A maimakon haka, APC ta ce hutun zai ba shi damar ɗan ja da baya daga yawan ayyukan yau da kullum domin ya huta, ya sake samun kuzari da kuma yin tunani kan manyan nauyin da ke gabansa.

Sanarwar ta ce Yilwatda zai yi amfani da lokacin wajen inganta tunaninsa na dabarun siyasa gabanin zaɓen 2027.

Jam’iyyar ta bayyana zaɓen a matsayin muhimmin lokaci ga makomar APC da kuma ajandar Renewed Hope ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ana shirin taron NWC

Ana kuma sa ran shugaban APC zai yi amfani da hutun wajen nazarin mataki na gaba na ci gaban jam’iyyar da kuma kammala shirye-shiryen wani taron Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa.

Taron zai bai wa NWC damar duba ci gaban da jam’iyyar ta samu, gano sababbin ƙalubalen da suka kunno kai da kuma cimma matsaya kan dabarun da za a bi a watannin da ke tafe.

Kara karanta wannan

Dan takarar shugaban kasa ya gano abin da ya hana a magance rashin tsaro a Najeriya

APC ta ce taron zai ƙara inganta haɗin gwiwa tsakanin mambobin NWC tare da ƙarfafa shirye-shiryen jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.

Shugaban APC zai je hutu
Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda Hoto: @OfficialAPCNg
Source: Twitter

Shugaban APC ya soki :yan adawa

A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar APC mai mulki ta yi watsi da sabon taron da manyan jam'iyyun adawa suka gudanar a Najeriya..

Shugaban APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya ce taron ya nuna fargabar da ke tattare da 'yan adawa kan abin da yake ganin zai zama mummunan shan kashi a babban zaben 2027.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng