Ministan Tinubu Ya Debo da Girma, Ya Ce ba Zai Bari Atiku Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa ba

Ministan Tinubu Ya Debo da Girma, Ya Ce ba Zai Bari Atiku Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa ba

  • Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya ce zai ci gaba da taka rawar gani a siyasar jihar Rivers gabanin zaben shugaban kasa na 2027
  • Tsohon gwamnan ya ce ba zai zauna ya rike hannu bibbiyu ya bar Atiku Abubakar ya lashe zaben shugaban kasa ba
  • Wike ya ce yawan zuwa jiharsa ta Rivers da yake yi ba yana nufin zai bari Abuja ya dawo gida ua zauna ba ne

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Port Harcourt, Rivers - Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya ce zai ci gaba da shiga harkokin siyasa a jihar Rivers gabanin zaben shugaban kasa na 2027.

Wike ya ce ba zai zauna ya rike hannu bibbiyu ya bar tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya lashe zaben shugaban kasar mai zuwa ba.

Wike Atiku.
Ministan birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar Hoto: Nyesom Wike, Atiku Abubakar
Source: UGC

Leadership ta ruwaito cewa Ministan ya bayyana hakan ne ranar Laraba, 2 ga watan Satumba, 2026 yayin ganawarsa da wasu zababbun manema labarai a Port Harcourt, jihar Rivers.

Kara karanta wannan

Tsohon gwamna ya fito ya fadi gaskiyar dalilin da ya sa yake neman mulkin Najeriya a 2027

Wike ya kuma yi watsi da rade-radin cewa yawan zuwansa jihar Rivers na nuna cewa yana shirin barin Abuja ya koma zama a jiharsa.

Dalilin Wike na yawan zuwa Rivers

Tsohon gwamnan jihar Rivers ya ce zuwansa jihar akai-akai na da alaka da bukatar ci gaba da tuntubar magoya bayansa tare da bibiyar abubuwan da ke faruwa a siyasance yayin da ake tunkarar zaben 2027.

Wike ya ce:

“Kuna so ne in zauna hannu bibbiyu Atiku Abubakar ya zo ya lashe zabe?”

Ya nace cewa yawan kasancewarsa a jihar Rivers ba yana nufin ya yi watsi da aikinsa na Ministan Abuja ko kuma yana shirin barin babban birnin tarayya ba ne.

Ya ce:

“Ba batun komawa zama ba ne, batun shi ne zuwa gida domin saduwa da jama’a, yin magana da su da kuma gudanar da abubuwan da kuka san kun iya yi sosai, ba tare da yin sakaci ba.

“Saboda haka, ba na dawo zama ba ne, ba na bukatar dawowa nan gida da zama, amma dole ne kuma in kasance tare da jama’ata domin kada kawai in zauna a Abuja ana gaya min cewa komai yana tafiya lafiya.”

Kara karanta wannan

Tinubu zai cigaba da aiki daga turai, babu zancen mika wa Kashim ragamar mulki

Wike zai bibiyi harkokin siyasa da kansa

Wike ya ce ba zai dogara kacokan kan tabbacin da abokan siyasarsa ke ba shi cewa komai yana tafiya daidai a jihar Rivers ba, kamar yadda Punch ta ruwaito.

Nyesom Wike.
Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Ezenwo Wike yana jawabi ga yan jarida a ofis Hoto: Nyesom Wike
Source: Facebook

Ya ce akwai bukatar ya rika zuwa jihar da kansa domin duba halin da ake ciki yayin da shirye-shiryen zaben 2027 ke kara kankama.

Ya ce:

“Ba na son in zauna a Abuja ’yan takara suna cewa, ‘Kada ka damu, komai yana tafiya lafiya.’ Dole ne in zo gida in gani da kaina cewa abubuwan suna tafiya yadda ya kamata. ‘Kun yi wannan? Yaya batun wancan?’”

Wike ya maida martani ga Peter Obi

A wani labarin, kun ji cewa Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya ce Shugaba Bola Tinubu ba shi da ikon tambayar yadda jihohi da ƙananan hukumomi ke kashe kudadensu.

Wike ya ce ya kamata Peter Obi ya tambayi yadda jihohi da ƙananan hukumomi ke amfani da kuɗaɗen da suke samu bayan cire tallafin mai

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262