Magana Ta Fito: An Bayyana Wadda Ta Yi Silar Hadakar Obi da Kwankwaso

Magana Ta Fito: An Bayyana Wadda Ta Yi Silar Hadakar Obi da Kwankwaso

  • KNN ta warware biri har wutsiya kan yadda aka kulla hadakar Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da Peter Obi
  • Kungiyar ta ce tattaunawar ta taimaka wajen zaburar da shirin kafa kawancen siyasa tsakanin Arewa da Kudu gabanin zaben 2027
  • KNN ta yi alkawarin tattara kuri’u miliyan biyar daga Kudu maso Gabas domin goyon bayan tikitin Obi da Kwankwaso

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Birnin Umuahia, Abia - Jagoran kungiyar Kwankwaso National Network (KNN) a shiyyar Kudu maso Gabas, Dr Ukpai Iro Ukpai, ya bayyana yadda wata magana daga Dr Aisha Rabiu Kwankwaso ta zaburar da kokarin hada mahaifinta, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, da Peter Obi.

Ukpai ya ce tattaunawar ta gudana ne a gidan Kwankwaso, inda Aisha ta tambayi mahaifinta dalilin da ya sa ba zai yi aiki tare da Obi ba.

Kara karanta wannan

Da gaske hukumar Hisbah ta hana Kiristoci gudanar da ibada a Sokoto

An yi magana kan hadakar Kwankwaso da Obi
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da Peter Obi a wajen taron jam'iyyar NDC Hoto: Hon. Saifullahi Hassan
Source: Facebook

Ukpai ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da jaridar Vanguard a birnin Umuahia na jihar Abia.

Ya ambato ta tana cewa:

“Daddy, me ya sa ba za ka tafi tare da wannan mutumin Obi ba?”

A cewar Ukpai, tambayar ta sa Kwankwaso yin la’akari da wata babbar hadaka ta kasa maimakon mayar da hankali kan bambancin yanki da burin siyasa.

KNN ta yaba wa Aisha Kwankwaso

Ukpai ya ce ya kamata a bai wa Aisha yabo da karramawa saboda rawar da ta taka wajen zaburar da wannan tunanin.

Ya bayyana Aisha, wadda sabuwar likita ce da ta kammala karatu, a matsayin wakiliyar matasa da kuma hadin kan kasa.

A cewarsa, ta ga yiwuwar hada hangen Obi kan tattalin arziki da kuma karfin Kwankwaso na samun goyon bayan jama’a a matakin kasa.

Ukpai ya ce tambayar Aisha ta nuna yadda matasan Najeriya ke kara neman shugabannin da za su hada kan al’umma ba tare da la’akari da bambancin kabila ko yanki ba.

Kara karanta wannan

Matar aure ta biyewa zuciya ta kona diyar mijinta da ruwan zafi

Ana neman gina kawancen Arewa da Kudu

Jagoran na KNN a Kudu maso Gabas ya ce bayan wannan tattaunawa, kokarin gina kawancen siyasa tsakanin Arewa da Kudu ya kara samun karfi.

Ya ce kungiyar KNN ta shiyyar Kudu maso Gabas ta amince da Aisha a matsayin memba na girmamawa saboda rawar da ta taka wajen zaburar da shirin hadin kan siyasa.

Ukpai ya ce kawancen Obi da Kwankwaso, idan aka kammala shi, zai iya zama babban karfi a zaben shugaban kasa na 2027.

KNN na neman kuri’u miliyan 5

Ukpai ya bayyana Kwankwaso a matsayin “mai mutane”, yana mai kwatanta tsarin siyasarsa da na marigayi dattijo Maitama Sule da marigayi Malam Aminu Kano.

A cewarsa, karfin Kwankwaso a Arewa da kuma goyon bayan Obi a Kudu, musamman tsakanin matasa, na iya samar da tubalin wata babbar kawancen kasa.

Ya ce KNN za ta ci gaba da tattara goyon baya a Kudu maso Gabas da sauran sassan Najeriya domin tabbatar da tsarin siyasar da take ganin zai karfafa hadin kan kasa.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban kasa ta sake gano lam'a a shirin Atiku na dawo da tallafin fetur

Ukpai ya ce kungiyar ta kuduri aniyar tattara kuri’u miliyan biyar daga Kudu maso Gabas domin goyon bayan tikitin hadin gwiwar Obi da Kwankwaso a zaben 2027.

Ya kara da cewa yakamata sauye-sauyen siyasar da ake samu gabanin zaben su dogara kan kwarewa, hadin kai da kuma kudurin magance matsalolin tattalin arziki da zamantakewa da ke addabar Najeriya.

Kwankwaso ya yi hadaka da Peter Obi
Madugun Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso Hoto: Hon. Saifullahi Hassan
Source: Facebook

Dickson ya gana da Kwankwaso, Obi

A wani labarin kuma, kun ji cewa jigon jam'iyyar NDC, Sanata Henry Seriake Dickson, ya yi kira ga mambobin jam'iyyar su haɗa kai domin tabbatar da nasarar 'yan takararta a zaben 2027.

Sanata Dickson ya yi kiran ne bayan tattaunawa da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar, Peter Obi, da wanda zai masa mataimaki, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng