Matar Aure Ta Biyewa Zuciya Ta Kona Diyar Mijinta da Ruwan Zafi

Matar Aure Ta Biyewa Zuciya Ta Kona Diyar Mijinta da Ruwan Zafi

  • An kai Zara Muhammad, wata mai shayarwa, asibiti bayan zargin matar mahaifinta ta kona ta da ruwan zafi a yankin Kofa da ke Maiduguri
  • Shaidu sun ce rikicin ya samo asali ne daga gardama tsakanin matan biyu, kafin lamarin ya rikide zuwa mummunan hari da ya jikkata Zara
  • Hukumar kula da harkokin mata ta Borno ta shiga tsakani, inda aka kai Zara asibiti domin samun kulawa, yayin da aka kama matar auren

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Borno - An kwantar da wata mai shayarwa, Zara Muhammad, a asibiti bayan zargin cewa matar mahaifinta ta kona ta da ruwan zafi a yankin Kofa da ke Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne ranar Lahadi, 23 ga watan Agustan 2026 bayan wata takaddama ta baki tsakanin matan biyu.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban kasa ta sake gano lam'a a shirin Atiku na dawo da tallafin fetur

Matar aure ta kona diyar mijinta
Taswirar jihar Borno, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Wata maƙwabciya, wadda ita ma aka bayyana sunanta da Zara, ta ce ihun wadda abin ya shafa ne ya sanar da mazauna yankin cewa akwai matsala, cewar rahoton jaridar Daily Trust.

Ta ce da ta garzaya gidan, ta tarar da matar gidan tana matsa Zara a kan ruwan zafin da ya zube a ƙasa.

“Na tsawata mata sannan na yi amfani da dukkan ƙarfina wajen raba ta da yarinyar. Abin takaici, ta riga ta samu munanan kuna kafin mu ceci ta,” in ji maƙwabciyar.

Zargin cin zarafi bayan samun ciki

Wasu mazauna yankin sun yi zargin cewa Zara ta fuskanci matsaloli tun bayan da ta samu ciki, bayan mutumin da ta yi hulɗa da shi ya yi watsi da ita.

Sun ce iyayenta sun taɓa matsa mata ta zubar da cikin, amma ta ƙi amincewa da hakan.

Mazauna yankin sun kuma yi zargin cewa bayan ta haifi ɗanta, ana tauye mata abinci tare da cin zarafinta a lokutan da rashin jituwa ya shiga tsakaninta da matar mahaifin nata.

Kara karanta wannan

Gwamna ya dauki zafi da yan bindiga suka kai mummunan hari masallaci ana cikin Sallah

Zara ta bayyana abin da ya faru

Da take bayyana abin da ya faru, Zara Muhammad ta ce matsalar ta fara ne bayan ɗiyarta ƙarama ta yi ƙoƙarin shiga ɗakin matar mahaifinta.

Ta ce matar gidan ta hana yarinyar shiga, lamarin da ya sa ta shiga tsakani domin ta ɗauki ɗiyarta ta tafi.

A cewarta, rashin jituwar ta ci gaba har na tsawon kwanaki uku, kafin matar mahaifin nata ta yi barazanar daina ba su abinci.

“Lokacin da na ce Allah zai azurta ni da ƙaramar ɗiyata, sai ta taso da sauri ta matsa ni cikin ruwan zafin da ta zubar a ƙasa,” in ji Zara.

An kai ta asibiti, an cafke matar gidan

Shaidu sun yi zargin cewa bayan harin, an bar Zara cikin azaba ba tare da samun isasshen kulawar lafiya ba.

Sai dai mahaifin Zara ya musanta zargin cewa an yi sakaci da ita ko kuma ana ƙoƙarin kare matarsa.

“Har an kai ta asibiti,” in ji shi.

Kara karanta wannan

Masana'antar fim ta yi rashi, fitaccen jarumi a Najeriya ya bar duniya

Bayan shiga tsakani da Kwamishiniyar Harkokin Mata ta Jihar Borno, Hajiya Zuweira Gambo, wata tawagar agaji ta dauki Zara zuwa wata cibiyar lafiya domin yi mata magani.

A halin yanzu, jami’an tsaro sun kama matar gidan tare da tsare ta domin gudanar da bincike kan zargin da ake yi mata.

Matar aure ta kona yarinyar mijinta a Borno
Shugaban rundunar 'yan sandan Najeriya, Olatunji Disu Hoto: Nigeria Police Force
Source: Facebook

Matar aure ta halla mijinta

A wani labarin kuma, kun ji cewa wata mata mai suna Innocent Serah ta shiga hannun ’yan sanda bayan an zarge ta yin ajalin mijinta, Innocent Nwaoji.

Ana dai zargin matar ta soka wa mijinta, Innocent Nwaọjị, wuka har ya mutu a Umuokereke Ngwa, ƙaramar hukumar Obingwa ta jihar Abia.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng