"Ba Sabon Alkawari ba"; Abin da Gwamna Radda Zai Yi Kamfen da Shi a Katsina

"Ba Sabon Alkawari ba"; Abin da Gwamna Radda Zai Yi Kamfen da Shi a Katsina

  • Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda ya ce zai nemi wa’adi na biyu ne bisa ayyukan da gwamnatinsa ta gudanar, ba sababbin alkawura ba
  • Radda ya bayyana cewa dukkan mazabu 361 na jihar Katsina sun amfana da akalla wani aiki ko shiri na gwamnatinsa
  • Gwamnan ya bukaci shugabannin APC Zalla Movement su karfafa wayar da kan jama’a da kuma yakin neman zabe a matakin kasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Katsina - Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta nemi goyon bayan jama’a domin wa’adi na biyu ne bisa nasarorin da ta samu, maimakon yin sababbin alkawura.

Radda ya bayyana hakan ne ranar Juma’a, 21 ga watan Agustan 2026 yayin kaddamar da masu kula da APC Zalla Movement a kananan hukumomi 34 da mazabu 361 na jihar Katsina, a People’s Square da ke Katsina.

Kara karanta wannan

Hadimin gwamna ya saduda, ya fito ya ba Davido hakuri

Gwamna Radda zai yi kamfen
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

An shirya taron ne domin karfafa tsarin jam’iyyar a matakin kasa karkashin jagorancin marigayi Dr. Bala Nuhu Kankia, cewar rahoton tashar Channels tv.

Da me Radda zai yi yakin neman zabe?

Da yake jawabi ga ’yan jam’iyyar, gwamnan ya ce gwamnatinsa ta gudanar da ayyuka a sassa daban-daban na jihar, lamarin da ya sanya ta cikin kyakkyawan matsayi na neman sabon goyon bayan jama’a bisa abin da ta aikata.

“Yau, jama’a ba sa kallon alkawura kawai. A zabe mai zuwa, za mu nuna wa jama’a abin da muka yi, ba za mu yi sababbin alkawura ba,” in ji Gwamna Radda.

Ya ce kowace daga cikin mazabu 36 da ke jihar Katsina ta samu wani aiki ko tallafin gwamnati tun bayan da gwamnatinsa ta hau mulki.

“A cikin dukkan mazabu 361 na jihar Katsina, babu mazabar da ba ta da wani aiki da wannan gwamnati ta gudanar,” in ji shi.

Radda ya bukaci kara wayar da kai

Kara karanta wannan

Gwamnan Sokoto ya gaya wa mutane abin da za su yi a kawo karshen 'yan bindiga

Gwamna Radda ya bayyana kaddamar da shugabannin APC Zalla Movement a matsayin wani muhimmin mataki wajen karfafa hadin gwiwa tsakanin kungiyar da tsarin APC da ke akwai.

Ya bukaci sababbin masu kula da kungiyar da aka kaddamar da su kasance masu jajircewa, da’a da mayar da hankali wajen kara karfafa kasancewar jam’iyyar a matakin kasa.

Gwamnan ya kuma umurci shugabannin da su kara kaimi wajen wayar da kan jama’a, ta hanyar kai bayanai kan manufofi, shirye-shirye da nasarorin gwamnati kai tsaye ga al’ummomin sassan jihar.

Gwamnati za ta samar da motoci

Domin inganta ayyukan kungiyar, Radda ya sanar da cewa gwamnatinsa za ta samar da motoci ga shiyyoyin gudanarwa uku na APC Zalla Movement domin saukaka ayyukan hada jama’a da kai musu bayanai.

Ya kuma yi kira ga shugabannin jam’iyyar da magoya bayanta da su ci gaba da kasancewa cikin hadin kai wajen kare wa’adin da jama’a suka bai wa APC cikin yardarsu.

Gwamnan ya tabbatar musu da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da samar da ribar dimokuradiyya tare da neman shiriyar Allah wajen tafiyar da mulki.

Kara karanta wannan

Ainihin dalilin gwamna Nasir Idris na sauya mataimakinsa a 2027

Radda ya yi magana kan kamfen a 2027
Gwamna Dikko Umaru Radda na jawabi a wajen taro Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

Radda ya tuna marigayi Kankia

Gwamna Radda ya yi wa marigayi Dr. Bala Nuhu Kankia jaje da yabo bisa kafa APC Zalla Movement, inda ya bayyana shi a matsayin jigon jam’iyya mai biyayya wanda hangen nesansa ya taimaka wajen karfafa tsarin siyasar APC.

Ya ce yana da yakinin cewa fadada kungiyar zuwa matakin kananan hukumomi da mazabu zai kara karfafa aikin hada kan jama’a da wayar da kan al’umma a matakin kasa.

Sanata Goje ya musanta barin APC

A wani labarin kuma, kun ji cewa Sanata Danjuma Goje mai wakiltar Gombe ta Tsakiya, ya musanta batun ficewa daga jam'iyyar APC.

Sanata Danjuma Goje ya bayyana cewa yana ci gaba da tattaunawa da masu ruwa da tsaki, inda ya bukaci magoya bayansa su jira umarninsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng