Gwamnan Jihar Katsina
A labarin nan, za a ji cewa rundunar sojin Najeriya ta aika dakaru bayan an samu kiran gaggawa na cewa 'yan bindiga na shirin kai hari wani yankin Katsina.
Gwamnatin Katsina za ta raba Naira biliyan 4 ga mazabu 361, inda kowace za ta samu Naira miliyan 10 domin gudanar da ayyukan ci gaba bayan amincewar Gwamna Radda.
Yan bindiga sun kashe mutum 1 tare da sace mutane 31 a kauyen Shuwaki da ke karamar hukumar Bakori a Katsina, lamarin da ya kara tayar da hankalin mazauna yankin.
Wani alƙalin kotun Shari'a a jihar Katsina ya tsere ta taga bayan 'yan bindiga sun kai hari kotu suna neman shi, lamarin da ya sake tayar da hankalin mazauna yankin.
Masana sun ce zaben 2027 zai gwada karfin APC a Katsina bayan rasuwar Muhammadu Buhari, yayin da ake hasashen karin fafatawa tsakanin jam'iyyun siyasar jihar.
A labarin nan, za a ji cewa rundunar tsaron kasar nan ta kara samun gagarumar nasara wajen kakkabe ayyukan yan bindiga da suka kai hari jihar Katsina.
Yara 'yan uwa biyu sun mutu bayan ambaliya ta kwashe su a Janbago, yayin da iyaye da mazauna yankin suka roki gwamnatin jihar Katsina ta dauki mataki.
Jigon ADC a Katsina, Dr Mustapha Inuwa, ya ce gwamnonin APC uku sun ziyarce shi ne domin neman auren diyarsa a madadin Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima.
Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema ya bayyana cewa matakan da Shugaba Bola Tinubu ya dauka a Najeriya zun zama dole domin farfado da tattalin arziki.
Gwamnan Jihar Katsina
Samu kari