Osun 2026: Kananan Hukumomi 8 da Ka Iya Tasiri Wurin Samar da Mai Nasara a Zaɓen
- Zaben gwamnan Osun na ranar 15 ga Agusta ya fi karkata kan Adeleke, Oyebamiji da Salaam, wadanda duk suka fito daga Osun ta Yamma
- Osogbo, Olorunda, Ife Central, Ife ta Gabas, Ife ta Kudu, Odo Otin, Iwo da Ilesa ta Gabas na cikin manyan kananan hukumomin jihar
- Adeleke na dogaro da ayyukan raya kasa da karfin Ede, yayin da Oyebamiji da Salaam ke neman samun gagarumar nasara a wasu muhimman kananan hukumomi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Osogbo, Osun - A yau Asabar 15 ga watan Agustan 2026 ake gudanar da zaben gwamnan Osun takarar tsakanin gwamna mai ci Ademola Adeleke, Bola Oyebamiji da Najeem Salaam ta kara tsauri
Dukkan manyan ‘yan takarar uku sun fito daga mazabar Osun ta Yamma, lamarin da ya sa rabon kuri’u ke iya zama mai matukar zafi.

Source: Twitter
Yankin da Adeleke da Salaam suka fito
Adeleke da Salaam sun fito daga mazabar tarayya ta Ede ta Arewa, Ede ta Kudu, Egbedore da Ejigbo, yayin da Oyebamiji ya fito daga Irewole, Isokan da Ayedaade, cewar Punch.
Adeleke na dogaro da ayyukan raya kasa da gwamnatinsa ta aiwatar cikin shekaru hudu domin samun kuri’un jama’a musamman daga Ede da makwabtanta
Mataimakinsa Kola Adewusi da tsohon sakataren PDP na kasa, Farfesa Wale Oladipo, na kokarin kara masa kuri’u a Ife Central, Ife ta Gabas da Ife ta Kudu
Tsohon SSG na Osun, Moshood Adeoti, wanda ya fito daga Iwo, shi ma yana kokarin taimakawa Adeleke wajen samun nasara a mazabar Iwo.

Source: Instagram
Osun: Abin da ka iya rage tasirin Adeleke
Sai dai kasancewar mataimakin Oyebamiji, Benjamin Adereti, dan Ile-Ife ne na iya rage karfin Adeleke a kananan hukumomin Ife uku
Dan takarar APC na Sanata, Amos Ogunbiyi, na iya zama cikas ga Adeleke a Iwo, yayin da goyon bayan Iyiola Omisore zai iya taimaka wa Oyebamiji.
Oyebamiji na sa ran samun kuri’u masu yawa a mazabarsa, inda tsohon dan takarar gwamna, Dotun Babayemi, ke kokarin taimaka masa a yankin Gbongan.
Goyon bayan bangaren PDP karkashin tsohon gwamna Olagunsoye Oyinlola na iya kara karfin Oyebamiji a Odo Otin, yayin da ake sa ran ya yi karfi a Boluwaduro.
Oyebamiji ana ganin zai yi karfi a Boripe, Irepodun, Ife ta Arewa da Obokun, yankunan da ke da alaka da tsohon gwamna Adegboyega Oyetola.

Source: Original
Tasirin da Saalam zai iya yi a zaɓen
Najeem Salaam, tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Osun na tsawon shekaru takwas, na ci gaba da kasancewa dan takara mai karfin gaske a zaben.
Baya ga Ejigbo, inda yake da karfi, ana sa ran Salaam zai yi kyau a Ilesa ta Gabas, Osogbo da Olorunda saboda tasirin tsohon gwamna Rauf Aregbesola.
Sai dai alakar Salaam da Aregbesola na iya zama kalubale, musamman wajen samun karin karbuwa a wasu sassan Osun.
Osun: Kananan hukumomi da ka iya yin tasiri
Ban da manyan ƙananan hukumomin yan takarar gwamna a zaɓen, ana ganin waɗannan ƙananan hukumomi za su taka rawa wajen yanke wanda zai yi nasara.
Wasu daga cikin ƙananan hukumomin da ake ganin suna da tasiri sun haɗa da:
Olorunda
Ife ta Tsakiya
Ife ta Gabas
Ife ta Kudu
Odo Otin
Iwo
Ilesa ta Gabas
Gwamna Adeleke ya zargi tsohon gwamna Oyetola da amfani da karfin gwamnatin tarayya wajen kawo cikas ga yakin neman zabensa.
A wani muhawarar Arise TV, Adeleke ya ce an kama wasu ‘yan Accord, yayin da daya daga cikin ‘yan takarar jam’iyyar ke tsare a Abuja
Ya ce ya tuntubi Bishop Matthew Kukah domin shiga tsakani kafin ya amince da halartar taron sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.
Dabarar da APC ke yi kan zaben Osun
A baya, mun ba ku labarin cewa shugaban masu rinjaye na majalisar dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele, ya bayyana cewa APC za ta lashe zaben gwamnan jihar Osun.
Sanata Opeyemi Bamidele ya bayyana cewa APC za ta lashe zaben ne ta hanyar tsarin siyasarta, ba tare da dogaro da tasirin gwamnatin tarayya ba.
Hakan na zuwa ne yayin ake fafatawa a zaben gwamnan Osun a yau Asabar 15 ga watan Agustan shekarar 2027 wanda ake ganin za ta yi matukar zafi musamman tsakanin Accord, APC da kuma ADC.
Asali: Legit.ng


