Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamnan Jihar Osun ke Gudana, Accord, APC da ADC Sun Ja Daga

All posts
Key Events
Analysis
Exclusive
2 Posts
Sort by
Ahmad Yusuf avatar
daga Ahmad Yusuf

INEC ta fara raba kayan zabe

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta fara jigilar kayayyakin zabe masu muhimmanci zuwa daukacin kananan hukumomi 30 na Jihar Osun tun a ranar Alhamis.

An samu tsaiko wajen rarraba kayayyakin ne biyo bayan umarnin kotu da ya haifar da sake buga takardun zabe domin shigar da dan takarar jam'iyyar SDP.

Ahmad Yusuf avatar
daga Ahmad Yusuf

Mutum miliyan 1.9 sun karbi katin zabe

INEC ta bayyana cewa sama da katunan zaɓe (PVCs) miliyan 1.9 aka karɓa domin zaɓen gwamnan jihar Osun da zai gudana yau Asabar.

Hukumar zaben mai zaman kanta ta dauki alkawarin gudanar da zabe mai inganci, sahihi kuma cikin kwanciyar hankali.