live
Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamnan Jihar Osun ke Gudana, Accord, APC da ADC Sun Ja Daga
All posts
Key Events
Analysis
Exclusive
INEC ta fara raba kayan zabe
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta fara jigilar kayayyakin zabe masu muhimmanci zuwa daukacin kananan hukumomi 30 na Jihar Osun tun a ranar Alhamis.
An samu tsaiko wajen rarraba kayayyakin ne biyo bayan umarnin kotu da ya haifar da sake buga takardun zabe domin shigar da dan takarar jam'iyyar SDP.
Mutum miliyan 1.9 sun karbi katin zabe
INEC ta bayyana cewa sama da katunan zaɓe (PVCs) miliyan 1.9 aka karɓa domin zaɓen gwamnan jihar Osun da zai gudana yau Asabar.
Hukumar zaben mai zaman kanta ta dauki alkawarin gudanar da zabe mai inganci, sahihi kuma cikin kwanciyar hankali.
Back to top