Abin Boye Ya Fito: 'Hanyar da APC Za Ta Bi don Lashe Zaben Gwamnan Osun'
- Shugaban masu rinjaye a Majalisar Dattawa, Opeyemi Bamidele, ya bayyana hanyar da APC za ta lashe zaben gwamnan Osun na 15 ga Agustan 2026
- Bamidele ya ce APC ta fi hadin kai da tsari tun bayan kayen da ta sha a zaben 2022, yayin da ya ce tsarin siyasar Gwamna Ademola Adeleke ya samu tangarda
- Sanatan ya bukaci ’yan siyasa da mazauna Osun su mutunta dokokin zabe tare da guje wa tashin hankali domin a gudanar da zaben cikin lumana
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Osun - Shugaban masu rinjaye a Majalisar Dattawa, Opeyemi Bamidele, ya yi magana kan hanyar da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) za ta lashe zaben gwamnan Jihar Osun da za a gudanar ranar 15 ga Agustan 2026.
Sanata Opeyemi Bamidele ya bayyana cewa APC za ta lashe zaben ne ta hanyar tsarin siyasarta, ba tare da dogaro da tasirin gwamnatin tarayya ba.

Source: Facebook
Jaridar TheCable ta ce Bamidele ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, 12 ga watan Agustan 2026, inda ya kuma yi kira ga ’yan siyasa da mazauna jihar da su tabbatar da an gudanar da zaben cikin lumana.
Bamidele ya hango nasarar APC
Ya yi watsi da ikirarin Gwamnan Osun, Ademola Adeleke, cewa APC na dogaro da karfin gwamnatin tarayya domin kayar da shi.
Sanatan ya ce jam’iyyar ta kara samun hadin kai da tsari tun bayan kayen da ta sha a zaben 2022.
A cewar Bamidele, ingantaccen tsarin APC, tare da abin da ya bayyana a matsayin lalacewar alakar Adeleke da wasu abokan siyasarsa, sun bai wa jam’iyyar damar yin nasara.
“Sabanin shekarar 2022, APC ta Osun a yanzu ta fi hadin kai da shiri, ba wai kawai domin ta dawo da ikon siyasar jihar ba, har ma domin sake tsara ta, ta yadda za ta amfani al’ummomin da za su zo nan gaba.”
“Ba za a iya fadar haka kan tsarin siyasar Adeleke ba, wanda ya shiga cikin rikici a tsakiyar wa’adinsa na farko.” In ji shi
Karfin siyasa ya fi mukami
Bamidele ya ce bai kamata a hada tsarin siyasa da kasancewa a kan mulki ba, yana mai cewa hanyar sadarwar jam’iyya a matakin kasa, karfin siyasa da alakar da take da masu zabe na daga cikin muhimman abubuwan da ke tabbatar da nasarar zabe.
“Karfin tasirin siyasa ne ke lashe zabe, ba karfin kasancewa kan mulki ba. Wannan na daga cikin manyan abubuwan da yanzu suka sanya APC cikin kyakkyawan matsayi na lashe zaben gwamna mai zuwa a Jihar Osun.” In ji shi.
Ya kawo sauya sheka da wasu jiga-jigan siyasa suka yi daga bangaren Adeleke zuwa APC a matsayin shaida kan karuwar karfin jam’iyyar.
Bamidele ya ambaci Francis Fadahunsi, sanatan da ke wakiltar Osun ta Gabas, da kuma ’yan majalisar wakilai uku, Omirin Olusanya, Wole Oke da Taofeek Ajilesoro, a matsayin ’yan siyasar da suka fice daga tsarin siyasar Adeleke. Ya ce ficewarsu ya kara karfin APC a matakin kasa gabanin zaben.
An bukaci a guji tashin hankali
Shugaban masu rinjayen Majalisar Dattawa ya bukaci dukkan jam’iyyu da ’yan takara da su mutunta dokokin zabe tare da mayar da hankali wajen gabatar da shirye-shiryensu ga masu zabe.
"A karshe, jama’a ne, ba gwamnatin tarayya ba, za su yanke shawarar wanda zai shugabance su.” In ji shi.

Source: Twitter
Abin da zai hana dan takarar ADC rashin nasara a Osun
A wani labarin kuma, kun ji cewa sakataren yaɗa labaran ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya bayyana kwarin gwiwar cewa ɗan takarar jam’iyyar a zaben gwamnan Osun, Najeem Salaam, zai yi nasara.
Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa za a samu matsalar rashin nasara ne idan ba a yi zaben a cikin gaskiya da nasara kamar yadda ake fargaba.
Asali: Legit.ng


