Abubuwa 3 da za Su Iya Sa Gwamna Adeleke Doke APC a Zaben Osun

Abubuwa 3 da za Su Iya Sa Gwamna Adeleke Doke APC a Zaben Osun

  • Gwamna Ademola Adeleke ya tsaya takara a karkashin jam'iyyar Accord bayan ya bar jam'iyyar PDP sakamakon rikicin cikin gida na jam'iyyar
  • Binciken ra'ayi na GSI ya bayyana cewa Adeleke yana da kusan kashi 79 na goyon baya idan aka kwatanta da kashi 15 na Bola Oyebamiji na APC
  • Masu tsokaci suna nuni da ayyukan hanyoyi, gyaran makarantu, da bayanan biyan albashi a matsayin muhimman abubuwan da za su taimakawa Adeleke

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Osun - Ana ganin Gwamnan Jihar Osun Ademola Adeleke a matsayin wanda yake kan gaba gabanin zaben gwamnan da za a yi a ranar 15 ga Agusta, 2026.

Ya tsayawa takara ne a karkashin tutar jam'iyyar Accord bayan ya bar jam'iyyar PDP a lokacin rikicin cikin gida na jam'iyyar.

Kara karanta wannan

Osun 2026: Muhimman abubuwa 8 da ya kamata kowane mai katin zabe ya sani

Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun
Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke. Hoto: Osun State Government
Source: Instagram

A wannan rahton, Legit Hausa ta tattaro muku wasu muhimman abubuwa da ake gani za su taimaka masa wajen cin nasara a zaben.

1. Ayyukan Adeleke a Osun

Gwamnatin Adeleke ta nuna kusan kilomita 350 na hanyoyin da aka gina ko aka gyara, sanya da fitilun kan hanya masu amfani da hasken rana, da aiki a kan hanyoyin da aka dade ana watsi da su a fadin jihar.

Fiye da makarantu 150 da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko fiye da 200 ne aka gyara a karkashin kulawarsa, kuma an kafa Jami'ar Ilesa a lokacin mulkinsa.

A bangaren jin dadin jama'a, gwamnatinsa ta yi ikirarin biyan albashi a kan lokaci, aiwatar da mafi karancin albashi mai tsoka, da kuma biyan muhimman sassa na bashin fansho da aka gada da kuma tulin basussukan jihar.

Ana ganin hakan na cikin abubuwan da za su taimaka wa gwamnan samun nasara a kan jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya.

Kara karanta wannan

Makinde: 'Dan takarar shugaban kasa ya samo mafita ga 'yan adawa gabanin 2027

2. Yawan mabiya a Osun

Adeleke yana rike da ingantaccen tsarin siyasa da ya ke aiki da shi bayan fitarsa daga jam'iyyar PDP.

Yana da rinjaye na musamman a Osun ta Yamma, musamman a Ede, yankin garinsu, inda ya samu goyon baya sosai a zaben 2022.

Goyon baya daga kungiyoyin kwadago, rundunonin tsaro na gargajiya, da kungiyoyin daban-daban sun kara karfafa Adeleke, kuma janyewar a kalla dan takarar hamayya guda daya daga APM ta kara rage yawan 'yan takara.

Tattausar muryar dan uwansa, tauraron kade-kade Davido, ta fito fili ta marawa yakin neman zabensa baya, lamarin da masu lura ke cewa zai iya kara fitowar matasa masu zabe.

Ademola Adeleke da Davido
Mawaki Davido tare da Ademola Adeleke. Hoto: Davido
Source: Instagram

3. Tasirin 'yan hamayya a Osun

APC ta kasance tana fuskantar kalubale a Osun duk da taimakon albarkatun gwamnatin tarayya, tsarin gwamnatin Tinubu, da kuma tasirin tsohon gwamna Gboyega Oyetola.

Legit ta rahoto cewa wasu masu hasashe na ganin gwamna Adeleke zai iya cin zabe lura da cewa 'yan jihar sun kasance karkashin jam'iyyar adawa lokaci mai tsawo.

Kara karanta wannan

2027: Abin da babban jami'in Birtaniya ya tattauna da Atiku a Abuja

Ana sayen kuri'u a Osun

Ana wani rahoton, mun kawo muku cewa an zargi jam'iyyun APC da Accord da shiga cikin harkallar sayen kuri'u a fadin Jihar Osun.

Hakan na zuwa ne yayin da wakilan jam'iyyun biyu ke ba masu zabe tsakanin N10,000 zuwa N20,000 gabannin zaben gwamna na yau.

Wata majiya ta tattaro cewa, wannan zaben ya bambanta da zabuka na baya saboda sayen kuri'un ya fara ne kwanaki shida gabanin zaben.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng