ADC: 'Abu 1 da zai Hana Jam'iyyar Su Atiku Nasara a Zaɓen Osun'
- Sakataren yaɗa labaran ADC, Bolaji Abdullahi, ya ce jam’iyyar na da kwarin gwiwar lashe zaben gwamnan Osun da za a gudanar a ƙarshen mako
- Bolaji Abdullahi ya nuna damuwa kan yawan jami’an soji da sauran jami’an tsaro da aka jibge a Osun, yana cewa hakan na iya jefa shakku kan sahihancin zaben
- Ya ce ADC ta yi imanin za ta iya kayar da Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027, ko da kuwa ba a samu haɗin kan dukkan jam’iyyun adawa ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Osun – Sakataren yaɗa labaran ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya bayyana kwarin gwiwar cewa ɗan takarar jam’iyyar a zaben gwamnan Osun, Najeem Salaam, zai yi nasara.
Bolaji Abdullahi ya ce abin da ya gani yayin wata ziyara da ya kai Osogbo kwanaki uku da suka gabata ya ƙara masa kwarin gwiwar cewa ADC na da gagarumar damar lashe zaben.

Source: Facebook
Arise News ta wallafa cewa za a samu matsalar rashin nasara ne idan ba a yi zaben a cikin gaskiya da nasara kamar yadda ake fargaba.
ADC ta yi magana kan zaben Osun
Jaridar Punch ta ruwaio cewa a lokacin da ya ziyarci Osogboo, ya samu kwarin gwiwa da ya tabbatar masa cewa ADC ce a kan gaba a jihar Osun.
A kalamansa:
“Na kasance cikin tawagar da ta ziyarci Osogbo kwanaki uku da suka gabata. Kafin mu je Osogbo, ina da damuwa kan ko da gaske muna da damar fafatawa wajen neman mulki a Osun a zaben wannan makon. Amma abin da na gani a Osogbo ya ƙara mini kwarin gwiwa cewa idan za a gudanar da zaben cikin ’yanci da adalci, ADC za ta lashe zaben."
Sai dai ya nuna damuwa kan abin da ya kira mayar da siyasar jihar Osun tamkar filin soja, yana cewa yawan jami’an soji da sauran jami’an tsaro da aka tura jihar na iya jefa shakku kan sahihancin zaben.

Kara karanta wannan
Sanatocin APC sun jajubo rigima da jam'iyyar, an ba su wa'adi su gyara alaka da ita
Abin da jama'ar Osun ke dubawa
Bolaji Abdullahi ya ce masu kada kuri’a za su fi duba shirin ɗan takarar na magance matsalolinsu, musamman batun samar da ayyukan yi da jin dadin ’yan fansho, maimakon yadda yake magana da Turanci.

Source: Twitter
Ya bayyana cewa:
“Mutanen Osun ba za su zabe shi ba saboda yana iya magana da wani irin Turanci. Za su zabe shi ne saboda yana iya magana kan bukatun da suke da su."
Ya kuma ce ba daidai ba ne a yi amfani da sakamakon zabukan baya wajen tantance karfin ADC a Osun, saboda zabukan da ake gudanarwa ba tare da babban zaben kasa ba suna da nasu musamman.
Atiku ya gargadi INEC kan zaben Osun
A baya, kun samu labarin cewa Atiku Abubakar ya gargadi INEC da hukumomin tsaro kan yawaita jami’an tsaro a zaben gwamnan Osun, yana mai cewa zaben gwaji ne ga Najeriya.
Atiku wanda shi ne 'dan takarar shugaban kasa na ADC ya ce zabe aikin farar hula ne, ba aikin soja ba, yana mai neman a tabbatar da gaskiya da adalci duba da abubuwan da ke faruwa.
Dan takarar shugaban kasar da ke fatan kifar da Bola Tinubu ya kuma bukaci a fayyace bambance-bambancen da aka ruwaito a takardar shaidar karatun shugaba mai ci da aka gabatar wa INEC.
Asali: Legit.ng
