Zaben Osun: Saura Kwana 5 a Kada Kuri'a, an Bankado Makarkashiyar da Ake Kullawa

Zaben Osun: Saura Kwana 5 a Kada Kuri'a, an Bankado Makarkashiyar da Ake Kullawa

  • Kwamitin yakin neman zaɓen Imole ya zargi jam’iyyar APC da ƙoƙarin matsa wa INEC lamba domin dakatar da zaɓe da tsakar rana a wasu sassan jihar Osun
  • Ya ce matakin na iya hana masu zaɓe a yankunan da ake ganin su ne cibiyoyin goyon bayan Gwamna Ademola Adeleke damar kaɗa ƙuri’a
  • Kwamitin ya buƙaci INEC da masu sa ido kan zaɓe su tabbatar da cewa an gudanar da zaɓen gwamna na ranar 15 ga Agusta cikin gaskiya da adalci

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Osun - Kwamitin yakin neman zaɓen Imole ya yi zargin cewa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na shirin matsa wa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) lamba.

Kwamitin ya ce ana shirin matsawa INEC lamba ne domin dakatar da kaɗa ƙuri’a da ƙarfe 12:00 na rana a wasu sassan jihar Osun yayin zaɓen gwamna na ranar 15 ga Agustan 2026.

Kara karanta wannan

"Za ka sha kaye"; Dan takarar ADC ya yi wa Gwamna Abba barazana kan zaben 2027

An yi zargi kan zaben jihar Osun
Gwamna Ademola Adeleke a wajen yakin neman zabe Hoto: Pelumi Olajengbesi
Source: Facebook

Kwamitin ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da kakakinsa, Pelumi Olajengbesi, ya fitar ranar Litinin, 10 ga watan Agustan 2026 a shafinsa na Facebook.

A cewar kwamitin, zargin shirin ya shafi ƙananan hukumomin da ake ganin su ne cibiyoyin siyasar Gwamna Ademola Adeleke.

Zargin hana mutane zaɓe

Kwamitin ya ce manufar matakin ita ce rage yawan ƙuri’un da za a samu tare da hana wasu masu kaɗa ƙuri’a da suka cancanta damar yin amfani da haƙƙinsu.

Sanarwar ta ce:

"Dole ne a bar al’ummar jihar Osun su yi amfani da haƙƙinsu na kundin tsarin mulki na zaɓe cikin ’yanci da lumana ba tare da tangarda, tsoratarwa ko hana su damar kaɗa ƙuri’a da gangan ba.”

Kwamitin ya buƙaci INEC ta yi watsi da duk wata matsin lamba ta siyasa tare da bin ƙa’idojin zaɓe da lokutan da aka tanada yayin gudanar da zaɓen.

Kara karanta wannan

'Dalilin da ya kamata ya sanya hukumar INEC ta gudanar da zaben 2027 a rana guda'

Sanarwar ta ci gaba da cewa:

“Bai kamata a rufe kowace rumfar zaɓe ba bisa son rai yayin da masu zaɓe da suka cancanta, waɗanda suka isa cikin lokacin da aka tanada, suke jiran su yi amfani da haƙƙinsu na zaɓe.”

An zargi APC da matsin lamba

Kwamitin ya kuma zargi APC da yin yunƙurin hana Adeleke da jam’iyyarsa shiga cikin jerin sunayen ’yan takara ta hanyar ƙalubalen shari’a a baya.

Haka kuma, ya zargi jam’iyyar da komawa ga amfani da kama mutane, tsoratarwa da muzgunawa mambobin Accord Party ta hannun ’yan sanda.

A cewar kwamitin, zargin ƙoƙarin yin tasiri kan INEC wani sabon yunƙuri ne na lalata tsarin zaɓe bayan matakan da aka ɗauka a baya, waɗanda ake zargin sun gaza rage goyon bayan da gwamnan ke samu.

Sai dai kwamitin bai gabatar da cikakkun bayanan sirrin da ya ce suka zama tushen wannan zargi ba.

An yi zargi kan zaben gwamnan Osun
Taswirar jihar Osun, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Dan takarar APC ya samu goyon baya a Osun

Kara karanta wannan

An kashe mutane 18 ana saura kwana 6 zaben gwamna, APC ta rasa mambobi 10

A wani labarin kuma, kun ji cewa ɗan takarar APGAa zaben gwamnan jihar Osun, Adesina Adeyemi-Doro, ya janye daga takarar tare da bayyana goyon bayansa ga ɗan takarar APC, Bola Oyebamiji.

Adeyemi-Doro ya bayyana matsayinsa ne yayin wani taro mai taken wanda kwamitin yaƙin neman zaɓen APC ya shirya a Osogbo.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng