APC Ta Wawushe Magoya bayan PDP da ADC, Gwamna Radda Ya Karbi Masu Sauya Sheka
- Gwamna Malam Dikko Radda ya karɓi ’yan siyasa da magoya bayan PDP da ADC da suka sauya sheka zuwa APC a Katsina
- ’Yan siyasar daga ƙaramar hukumar Safana sun ce ayyukan raya ƙasa da salon shugabancin gwamnan ne suka sa suka koma APC
- Sauya shekar na zuwa ne yayin da ake samun sauye-sauyen siyasa a Katsina gabanin kakar zaɓen 2027
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Katsina - Guguwar sauya sheka da ke sake fasalin siyasar jihar Katsina ta ƙara ƙarfi yayin da Gwamna Malam Dikko Radda ya karɓi wasu ’yan siyasa da magoya bayan PDP da ADC da suka koma jam'iyyar APC.
Mataimakin kakakin Majalisar Dokokin Jihar Katsina, Rt. Hon. Abduljalal Haruna Runka, tare da shugaban ƙaramar hukumar Safana, Hon. Abdullahi Sani (Brazil), ne suka gabatar da waɗanda suka sauya shekan ga gwamnan a gidan gwamnati da ke Katsina.

Source: Facebook
Sakataren yada labaran gwamnan Katsina, Ibrahima Kaulaha Mohammed, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a shafinsa na Facebook a ranar Litinin, 10 ga watan Agustan 2026.
Radda ya yi maraba da sabbin ’yan APC
Da yake maraba da sabbin ’yan jam’iyyar a ɗakin taro na majalisar gidan gwamnati da ke Katsina, Gwamna Radda ya bayyana cewa komawarsu APC alama ce ta amincewarsu da shugabancinsa da kuma ƙoƙarinsa na raya jihar Katsina.
“Mun yi farin cikin karɓar ku cikin APC. Matakin da kuka ɗauka ya nuna amincewarku da shugabancinmu da kuma ƙudurinmu na raya jihar Katsina,” in ji gwamnan.
Ya tabbatar wa al’ummar Safana cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiwatar da ayyuka da shirye-shiryen da za su inganta rayuwarsu.
Gwamnan ya kuma buƙaci tsofaffin ’yan jam’iyyar da sababbin waɗanda suka shigo da su kasance masu haɗin kai wajen ciyar da manufofin jam’iyyar gaba.
Mataimakin kakakin majalisa ya yi magana

Kara karanta wannan
2027: Matawalle ya fito fili ya bayyana irin zaben da za a yi karkashin gwamnatin Tinubu
Da yake gabatar da waɗanda suka sauya sheka, Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Katsina, Abduljalal Haruna Runka, ya ce tawagar ta zo ne domin sake tabbatar da amincewarta da APC a hukumance.
Ya kuma gode wa Gwamna Radda kan dimbin ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ta aiwatar a faɗin ƙaramar hukumar Safana.
“Muna godiya ga mai girma gwamna bisa tallafi da ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ta kawo wa al’ummarmu. Muna tabbatar masa da ci gaba da ba shi goyon baya da biyayya,” in ji shi.
Shi ma shugaban ƙaramar hukumar Safana, Hon. Abdullahi Sani, ya yi alƙawarin cewa masu ruwa da tsaki a siyasar yankin za su ci gaba da aiki tare domin ƙarfafa APC da kuma mara wa ajandar ci gaban gwamnan baya.
Dalilin da ya sa suka bar PDP
Da yake magana a madadin tsofaffin ’yan PDP, Umar Ya’u ya ce adalcin Gwamna Radda, salon shugabancinsa da ke bai wa kowa dama da kuma ayyukan raya ƙasa da ya gudanar ne suka sa suka bar jam’iyyar adawa.
Ya tuna cewa ya amfana da shirin gwamnatin jihar na sayar da taki mai tallafi a lokacin da yake ɗan PDP, yana mai cewa hakan ya nuna cewa gwamnan ba ya nuna bambanci wajen tallafa wa jama’a.

Kara karanta wannan
ADC ta kasa sasanta rikicinta a Katsina, manyan jiga jigai 2 sun fice daga cikinta
'Yan ADC sun bayyana dalilin komawa APC
Da yake magana a madadin waɗanda suka sauya sheka daga ADC, Hon. Umme Yakubu Safana, ya ce sun shiga APC ne saboda amincewarsu da shugabancin Gwamna Radda da hangen nesansa ga jihar.
“Mun yi farin cikin shiga APC kuma mu zama iyali guda. A shirye muke mu yi aiki tare da sauran ’yan jam’iyya kuma mu tallafa wa ci gaban jihar Katsina,” in ji shi.
Hon. Yahaya Abubakar (Dan Area) ne ya jagoranci tawagar PDP, yayin da Hon. Umme Yakubu Safana ya jagoranci tawagar ADC.

Source: Facebook
Dan takarar ADC ya kai kara kotu
A wani labarin kuma, kun ji cewa mai neman takarar gwamnan Nasarawa a inuwar ADC, Mohammed Hassan Abdullahi, ya kai karar jam'iyyar.
Tsohon Ministan muhallin ya kai kara kotu ne domin nuna rashin amincewa da zaben fitar da gwanin da ADC ta gudanar.
Asali: Legit.ng
