Ba kamar Tinubu ba, Peter Obi Ya Yi Ta Maza da Aka Nemi a Saki Takardun Karatunsa
- Peter Obi ya ce ba shi da wata matsala da Jami’ar Najeriya da ke Nsukka ta fitar da takardun digirinsa da sauran bayanan karatunsa
- Obi ya ce jami’ar ta ba shi digirin BA a Falsafa a shekarar 1984, kuma ya nemi a fitar da bayanan bisa doka idan an yi buƙatar hakan
- Ɗan takarar shugaban ƙasa na NDC ya ce ya yi amanna da gaskiya da riƙon amana, amma ya buƙaci a gudanar da binciken tarihin ’yan takara cikin adalci da bin doka
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Ɗan takarar shugaban ƙasa na NDC a zaɓen 2027, Peter Obi, ya nemi Jami’ar UNN da ke Nsukka ta fitar da bayanan karatunsa.
Peter Obi ya bukaci hakan ne bayan rahotannin daukar matakin shari’a da ke neman kwafin takardun karatunsa.

Source: Facebook
Obi ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Talata, 15 ga watan Satumban 2026.
Ya ce ba shi da wata matsala da a fitar da takardun digirinsa da sauran bayanan da suka shafi karatunsa a jami’ar.
Obi ya ce ya karɓi digirin Falsafa a 1984
Peter Obi ya ce Jami’ar Najeriya ta ba shi digirin Bachelor of Arts (BA) a fannin Falsafa a shekarar 1984.
Sanarwar tasa ta biyo bayan yaɗuwar rahotanni a kafafen sada zumunta game da wani mutum ko rukuni da ya ɗauki matakin shari’a domin neman kwafin takardar digirinsa da wasu bayanan da suka shafi karatunsa.
Obi ya ce ba shi da wata matsala kan fitar da waɗannan takardu.
“Ina son na bayyana karara cewa ba ni da wata adawa ko kaɗan da fitar da waɗannan bayanai,” in ji shi.
Ya nemi jami’ar ta fitar da bayanan bisa doka
Tsohon gwamnan na Anambra ya buƙaci Jami’ar UNN da ke Nsukka ta samar da takardun shaidar karatunsa, bayanansa da sauran takardun da suka shafi shigarsa jami’a da karatunsa, matuƙar an yi buƙatar hakan ta hanyar da doka ta amince da ita.
Ya kuma ce ba shi da wata adawa da hakan a sauran makarantun da ya halarta, a Najeriya da wajen ƙasar, kan su fitar da bayanan karatunsa bisa dokoki da ƙa’idojin da suka dace.
Obi ya ce yana maraba da binciken tarihinsa
Obi ya bayyana cewa ya yi imani sosai da gaskiya da riƙon amana, musamman ga mutanen da ke neman riƙe mukamin gwamnati.
Sai dai ya jaddada cewa ya kamata a gudanar da bincike kan ’yan takara cikin adalci, bisa doka kuma ba tare da nuna wariya ba.

Source: Facebook
Peter Obi ya ce bai ki karbar tayin Atiku ba
A wani labarin kuma, kun ji cewa Peter Obi, ya musanta rahotannin cewa ya ƙi karbar tayin zama abokin takarar Atiku Abubakar, ɗan takarar shugaban ƙasa na ADC, a zaɓen 2027.
Peter Obi ya ce ba a taɓa yi masa irin wannan tayin ba, don haka ba zai yiwu ya ƙi wata shawara da ba a gabatar masa da ita ba.
Asali: Legit.ng

